< Zabura 18 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
To the Overseer. — By a servant of Jehovah, by David, who hath spoken to Jehovah the words of this song in the day Jehovah delivered him from the hand of all his enemies, and from the hand of Saul, and he saith: — I love Thee, O Jehovah, my strength.
2 Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
Jehovah [is] my rock, and my bulwark, And my deliverer, My God [is] my rock, I trust in Him: My shield, and a horn of my salvation, My high tower.
3 Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
The 'Praised One' I call Jehovah, And from my enemies I am saved.
4 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
Compassed me have cords of death, And streams of the worthless make me afraid.
5 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol h7585)
Cords of Sheol have surrounded me, Before me have been snares of death. (Sheol h7585)
6 Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
In mine adversity I call Jehovah, And unto my God I cry. He heareth from His temple my voice, And My cry before Him cometh into His ears.
7 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
And shake and tremble doth the earth, And foundations of hills are troubled, And they shake — because He hath wrath.
8 Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
Gone up hath smoke by His nostrils, And fire from His mouth consumeth, Coals have been kindled by it.
9 Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
And He inclineth the heavens, and cometh down, And thick darkness [is] under His feet.
10 Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
And He rideth on a cherub, and doth fly, And He flieth on wings of wind.
11 Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
He maketh darkness His secret place, Round about Him His tabernacle, Darkness of waters, thick clouds of the skies.
12 daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
From the brightness over-against Him His thick clouds have passed on, Hail and coals of fire.
13 Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
And thunder in the heavens doth Jehovah, And the Most High giveth forth His voice, Hail and coals of fire.
14 Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
And He sendeth His arrows and scattereth them, And much lightning, and crusheth them.
15 Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
And seen are the streams of waters, And revealed are foundations of the earth. From Thy rebuke, O Jehovah, From the breath of the spirit of Thine anger.
16 Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
He sendeth from above — He taketh me, He draweth me out of many waters.
17 Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
He delivereth me from my strong enemy, And from those hating me, For they have been stronger than I.
18 Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
They go before me in a day of my calamity And Jehovah is for a support to me.
19 Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
And He bringeth me forth to a large place, He draweth me out, because He delighted in me.
20 Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
Jehovah doth recompense me According to my righteousness, According to the cleanness of my hands, He doth return to me.
21 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
For I have kept the ways of Jehovah, And have not done wickedly against my God.
22 Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
For all His judgments [are] before me, And His statutes I turn not from me.
23 Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
And I am perfect with him, And I keep myself from mine iniquity.
24 Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
And Jehovah doth return to me, According to my righteousness, According to the cleanness of my hands, Over-against his eyes.
25 Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
With the kind Thou showest Thyself kind, With a perfect man showest Thyself perfect.
26 ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
With the pure Thou showest Thyself pure, And with the perverse showest Thyself a wrestler,
27 Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
For Thou a poor people savest, And the eyes of the high causest to fall.
28 Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
For Thou — Thou lightest my lamp, Jehovah my God enlighteneth my darkness.
29 Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
For by Thee I run — a troop! And by my God I leap a wall.
30 Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
God! perfect [is] His way, The saying of Jehovah is tried, A shield [is] He to all those trusting in Him.
31 Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
For who [is] God besides Jehovah? And who [is] a rock save our God?
32 Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
God! who is girding me [with] strength, And He maketh perfect my way.
33 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
Making my feet like hinds, And on my high places causeth me to stand.
34 Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
Teaching my hands for battle, And a bow of brass was brought down by my arms.
35 Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
And Thou givest to me the shield of Thy salvation, And Thy right hand doth support me, And Thy lowliness maketh me great.
36 Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
Thou enlargest my step under me, And mine ankles have not slidden.
37 Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
I pursue mine enemies, and overtake them, And turn back not till they are consumed.
38 Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
I smite them, and they are not able to rise, They fall under my feet,
39 Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
And Thou girdest me [with] strength for battle, Causest my withstanders to bow under me.
40 Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
As to mine enemies — Thou hast given to me the neck, As to those hating me — I cut them off.
41 Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
They cry, and there is no saviour, On Jehovah, and He doth not answer them.
42 Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
And I beat them as dust before wind, As mire of the streets I empty them out.
43 Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
Thou dost deliver me From the strivings of the people, Thou placest me for a head of nations, A people I have not known do serve me.
44 da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
At the hearing of the ear they hearken to me, Sons of a stranger feign obedience to me,
45 Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
Sons of a stranger fade away, And are slain out of their close places.
46 Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
Jehovah liveth — and blessed [is] my rock, And exalted is the God of my salvation.
47 Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
God — who is giving vengeance to me, And He subdueth peoples under me,
48 wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
My deliverer from mine enemies, Above my withstanders Thou raisest me, From a man of violence dost deliver me.
49 Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
Therefore I confess Thee among nations, O Jehovah, And to Thy name I sing praise,
50 Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.
Magnifying the salvation of His king, And doing kindness to His anointed, To David, and to his seed — unto the age!

< Zabura 18 >