< Zabura 18 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
For the chief musician. A psalm of David, the servant of Yahweh, when he sang to Yahweh the words of this song on the day that Yahweh rescued him from the hand of all his enemies and from the hand of Saul. He sang: I love you, Yahweh, my strength.
2 Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
Yahweh is my rock, my fortress, the one who brings me to safety; he is my God, my rock; I take refuge in him. He is my shield, the horn of my salvation, and my stronghold.
3 Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
I will call on Yahweh who is worthy to be praised, and I will be saved from my enemies.
4 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
The cords of death surrounded me, and the rushing waters of worthlessness overwhelmed me.
5 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol )
The cords of Sheol surrounded me; the snares of death trapped me. (Sheol )
6 Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
In my distress I called to Yahweh; I called for help to my God. He heard my voice from his temple; my call for help went into his presence; it went into his ears.
7 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
Then the earth shook and trembled; the foundations of the mountains also trembled and were shaken because God was angry.
8 Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
Smoke went up from out of his nostrils, and blazing fire came out of his mouth. Coals were ignited by it.
9 Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
He opened the heavens and came down, and thick darkness was under his feet.
10 Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
He rode on a cherub and flew; he glided on the wings of the wind.
11 Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
He made darkness a tent around him, heavy rainclouds in the skies.
12 daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
Hailstones and coals of fire fell from the lightning before him.
13 Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
Yahweh thundered in the heavens! The voice of the Most High shouted.
14 Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
He shot his arrows and scattered his enemies; many lightning bolts dispersed them.
15 Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
Then the water channels appeared; the foundations of the world were laid bare at your rebuke, Yahweh, at the blast of the breath of your nostrils.
16 Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
He reached down from above; he took hold of me! He pulled me out of the surging water.
17 Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
He rescued me from my strong enemy, from those who hated me, for they were too strong for me.
18 Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
They came against me on the day of my distress but Yahweh was my support!
19 Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
He set me free in a wide open place; he saved me because he was pleased with me.
20 Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
Yahweh has rewarded me because of my righteousness; he has restored me because my hands were clean.
21 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
For I have kept the ways of Yahweh and have not wickedly turned away from my God.
22 Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
For all his righteous decrees have been before me; as for his statutes, I have not turned away from them.
23 Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
I have also been innocent before him, and I have kept myself from sin.
24 Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
Therefore Yahweh has restored me because of my righteousness, because my hands were clean before his eyes.
25 Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
To anyone who is faithful, you show yourself to be faithful; to a man who is blameless, you show yourself to be blameless.
26 ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
To anyone who is pure, you show yourself pure; but you are clever toward anyone who is twisted.
27 Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
For you save afflicted people, but you bring down those with proud, uplifted eyes!
28 Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
For you give light to my lamp; Yahweh my God lights up my darkness.
29 Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
For by you I can run over a barricade; by my God I can leap over a wall.
30 Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
As for God—his way is perfect! The word of Yahweh is pure! He is a shield to everyone who takes refuge in him.
31 Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
For who is God except Yahweh? Who is a rock except our God?
32 Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
It is God who puts strength on me like a belt, who places the blameless person on his path.
33 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
He makes my feet swift like a deer and places me on the heights!
34 Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
He trains my hands for war and my arms to bend a bow of bronze.
35 Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
You have given me the shield of your salvation. Your right hand has supported me, and your favor has made me great.
36 Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
You have made a wide place for my feet beneath me so that my feet have not slipped.
37 Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
I pursued my enemies and caught them; I did not turn back until they were destroyed.
38 Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
I smashed them so that they were unable to rise; they have fallen under my feet.
39 Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
For you put strength on me like a belt for battle; you put under me those who rise up against me.
40 Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
You gave me the back of my enemies' necks; I annihilated those who hated me.
41 Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
They called for help, but no one saved them; they called out to Yahweh, but he did not answer them.
42 Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
I beat them into fine pieces like dust before the wind; I threw them out like mud in the streets.
43 Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
You rescued me from the disputes of people. You have made me the head over nations. People that I have not known serve me.
44 da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
As soon as they heard of me, they obeyed me; foreigners were forced to bow to me.
45 Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
The foreigners came trembling out of their strongholds.
46 Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
Yahweh lives; may my rock be praised. May the God of my salvation be exalted.
47 Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
He is the God who executes vengeance for me, who subdues the nations under me.
48 wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
I am set free from my enemies! Indeed, you lifted me above the ones who rose against me! You rescued me from violent men.
49 Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
Therefore I will give thanks to you, Yahweh, among the nations; I will sing praises to your name!
50 Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.
God gives great victory to his king, and he shows his covenant loyalty to his anointed one, to David and to his descendants forever.