< Zabura 18 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
To him that excelleth. A Psalme of Dauid the seruant of the Lord, which spake unto the Lord the wordes of this song (in the day that the Lord delivered him for the hande of all this enemies, and form the and of saul) and sayd, I will loue thee dearely, O Lord my strength.
2 Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
The Lord is my rocke, and my fortresse, and he that deliuereth me, my God and my strength: in him will I trust, my shield, the horne also of my saluation, and my refuge.
3 Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
I will call vpon the Lord, which is worthie to be praysed: so shall I be safe from mine enemies.
4 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
The sorowes of death compassed me, and the floods of wickednes made me afraide.
5 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol )
The sorowes of the graue haue compassed me about: the snares of death ouertooke me. (Sheol )
6 Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
But in my trouble did I call vpon the Lord, and cryed vnto my God: he heard my voyce out of his Temple, and my crye did come before him, euen into his eares.
7 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
Then the earth trembled, and quaked: the foundations also of the mountaines mooued and shooke, because he was angrie.
8 Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
Smoke went out at his nostrels, and a consuming fire out of his mouth: coales were kindled thereat.
9 Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
He bowed the heauens also and came downe, and darkenes was vnder his feete.
10 Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
And he rode vpon Cherub and did flie, and he came flying vpon the wings of the winde.
11 Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
He made darkenes his secrete place, and his pauilion round about him, euen darkenesse of waters, and cloudes of the ayre.
12 daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
At the brightnes of his presence his clouds passed, haylestones and coles of fire.
13 Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
The Lord also thundred in the heauen, and the Highest gaue his voyce, haylestones and coales of fire.
14 Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
Then hee sent out his arrowes and scattred them, and he increased lightnings and destroyed them.
15 Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
And the chanels of waters were seene, and the foundations of the worlde were discouered at thy rebuking, O Lord, at the blasting of the breath of thy nostrels.
16 Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
He hath sent downe from aboue and taken mee: hee hath drawen mee out of many waters.
17 Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
He hath deliuered mee from my strong enemie, and from them which hate me: for they were too strong for me.
18 Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
They preuented me in the day of my calamitie: but the Lord was my stay.
19 Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
Hee brought mee foorth also into a large place: hee deliuered mee because hee fauoured me.
20 Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
The Lord rewarded me according to my righteousnes: according to the purenes of mine hands he recompensed me:
21 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
Because I kept the wayes of the Lord, and did not wickedly against my God.
22 Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
For all his Lawes were before mee, and I did not cast away his commandements from mee.
23 Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
I was vpright also with him, and haue kept me from my wickednes.
24 Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
Therefore the Lord rewarded me according to my righteousnesse, and according to the purenes of mine hands in his sight.
25 Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
With the godly thou wilt shewe thy selfe godly: with the vpright man thou wilt shew thy selfe vpright.
26 ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
With the pure thou wilt shewe thy selfe pure, and with the froward thou wilt shewe thy selfe froward.
27 Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
Thus thou wilt saue the poore people, and wilt cast downe the proude lookes.
28 Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
Surely thou wilt light my candle: the Lord my God wil lighten my darkenes.
29 Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
For by thee I haue broken through an hoste, and by my God I haue leaped ouer a wall.
30 Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
The way of God is vncorrupt: the worde of the Lord is tried in the fire: he is a shield to all that trust in him.
31 Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
For who is God besides the Lord? and who is mightie saue our God?
32 Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
God girdeth me with strength, and maketh my way vpright.
33 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
He maketh my feete like hindes feete, and setteth me vpon mine high places.
34 Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
He teacheth mine hands to fight: so that a bowe of brasse is broken with mine armes.
35 Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
Thou hast also giuen me the shield of thy saluation, and thy right hand hath stayed me, and thy louing kindenes hath caused me to increase.
36 Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
Thou hast enlarged my steps vnder mee, and mine heeles haue not slid.
37 Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
I haue pursued mine enemies, and taken them, and haue not turned againe till I had consumed them.
38 Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
I haue wounded them, that they were not able to rise: they are fallen vnder my feete.
39 Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
For thou hast girded me with strength to battell: them, that rose against me, thou hast subdued vnder me.
40 Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
And thou hast giuen me the neckes of mine enemies, that I might destroy them that hate me.
41 Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
They cryed but there was none to saue them, euen vnto the Lord, but hee answered them not.
42 Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
Then I did beate them small as the dust before the winde: I did treade them flat as the clay in the streetes.
43 Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
Thou hast deliuered me from the contentions of the people: thou hast made me the head of the heathen: a people, whom I haue not knowen, shall serue me.
44 da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
As soone as they heare, they shall obey me: the strangers shall be in subiection to me.
45 Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
Strangers shall shrinke away, and feare in their priuie chambers.
46 Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
Let the Lord liue, and blessed be my strength, and the God of my saluation be exalted.
47 Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
It is God that giueth me power to auenge me, and subdueth the people vnder me.
48 wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
O my deliuerer from mine enemies, euen thou hast set mee vp from them, that rose against me: thou hast deliuered mee from the cruell man.
49 Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
Therefore I will prayse thee, O Lord, among the nations, and wil sing vnto thy Name.
50 Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.
Great deliuerances giueth hee vnto his King, and sheweth mercie to his anoynted, euen to Dauid, and to his seede for euer.