< Zabura 18 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
To the music director. A psalm of David the servant of the Lord, who sang the words of this song to the Lord on the day when the Lord saved him from all his enemies, and from Saul. He sang: I love you, Lord. You are my strength.
2 Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
The Lord is my rock, my fortress, and my Savior. He is my God, my rock who protects me. He shields me from harm, his power protects me, he keeps me safe.
3 Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
I call for help from the Lord who should be praised, and he saves me from those who hate me.
4 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
Ropes of death encircled me, surging waters of destruction flooded over me;
5 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol )
The grave wound its ropes around me; death set snares for me. (Sheol )
6 Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
In my despair I called on the Lord—I cried out to my God for help. He heard my voice from his Temple—my cry for help reached his ears.
7 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
The earth shook to and fro; the foundations of the mountains trembled, shaking because of his anger.
8 Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
Smoke came out of his nostrils, and fire came from his mouth; burning coals blazed before him.
9 Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
He parted the heavens and came down, with dark clouds beneath his feet.
10 Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
Riding on an angel he flew, swooping on the wings of the wind.
11 Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
He hid himself in darkness, covering himself with black thunderclouds.
12 daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
Hailstones and burning coals flew out from his brightness, passing through his thick clouds.
13 Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
The Lord thundered from heaven; the voice of the Most High sounded among the hailstones and burning coals.
14 Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
He fired his arrows, scattering his enemies; he routed them with his lightning bolts.
15 Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
You roared, Lord, and by the wind from the breath of your nostrils the valleys of the sea were exposed and the foundations of the earth were uncovered.
16 Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
He reached down his hand from above and grabbed hold of me. He pulled me out of the deep water.
17 Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
He rescued me from my powerful enemies, from those who hated me and who were much stronger than me.
18 Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
They came at me at my worst possible moment, but the Lord supported me.
19 Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
He set me free, he rescued me because he's my friend.
20 Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
The Lord rewarded me because I do what's right; he repaid me because I am innocent.
21 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
For I have followed the Lord's ways; I have not sinned by turning away from my God.
22 Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
I have kept all his laws in mind; I have not ignored his commandments.
23 Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
I am blameless in his sight; I keep myself from sinning.
24 Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
The Lord rewarded me for doing what's right. I am innocent in his sight.
25 Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
You show trust to those who trust; you show integrity to those with integrity,
26 ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
You show yourself pure to those who are pure, but you show yourself smart to those who are crafty.
27 Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
You save the humble, but you bring down the proud.
28 Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
You light my lamp! Lord, my God, you light up my darkness!
29 Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
With you, I can charge down a troop of soldiers; with you, my God, I can climb a fortress wall.
30 Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
God's way is absolutely right. What the Lord says is trustworthy. He is a shield to all who come to him for protection.
31 Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
For who is God except the Lord? Who is the rock, except our God?
32 Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
God makes me strong and keeps me safe.
33 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
He makes me surefooted like the deer, able to walk the heights in safety.
34 Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
He teaches me how to fight in battle; he gives me the strength to draw a bronze bow.
35 Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
You protect me with the shield of your salvation; you support me with your powerful right hand; your help has made me great.
36 Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
You gave me space in which to walk, and prevented my feet from slipping.
37 Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
I chased my enemies, and caught up with them. I did not turn around until I had destroyed them.
38 Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
I struck them down—they couldn't get up. They fell at my feet.
39 Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
You made me strong for battle; you made those who rose up against me kneel down before me.
40 Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
You made my enemies run away; I destroyed all my enemies.
41 Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
They cried out for help, but no one came to rescue them. They even called out to the Lord, but he did not answer them.
42 Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
I ground them into dust, like dust in the wind. I threw them out like mud in the street.
43 Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
You rescued me from rebellious people; you made me ruler over nations—people I didn't know now serve me.
44 da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
As soon as they hear of me, they obey; foreigners cringe before me.
45 Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
They lose heart, and come trembling in surrender from their strongholds.
46 Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
The Lord lives! Blessed be my rock! May the God who saves me be praised!
47 Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
God avenges me, he subdues peoples under me,
48 wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
he rescues me from those who hate me. You keep me safe from those who rebel against me, you save me from violent men.
49 Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
That's why I will praise you among the nations, Lord; I will sing praises about who you are.
50 Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.
You have saved the king so often, showing your trustworthy love to David, your anointed, and to his descendants forever.