< Zabura 18 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
Unto the end, for David the servant of the Lord, who spoke to the Lord the words of this canticle, in the day that the Lord delivered him from the hands of all his enemies, and from the hand of Saul. I will love thee, O Lord, my strength:
2 Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
The Lord is my firmament, my refuge, and my deliverer. My God is my helper, and in him will I put my trust. My protector and the horn of my salvation, and my support.
3 Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
Praising I will call upon the Lord: and I shall be saved from my enemies.
4 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
The sorrows of death surrounded me: and the torrents of iniquity troubled me.
5 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol )
The sorrows of hell encompassed me: and the snares of death prevented me. (Sheol )
6 Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
In my affliction I called upon the Lord, and I cried to my God: And he heard my voice from his holy temple: and my cry before him came into his ears.
7 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
The earth shook and trembled: the foundations of the mountains were troubled and were moved, because he was angry with them.
8 Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
There went up a smoke in his wrath: and a fire flamed from his face: coals were kindled by it.
9 Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
He bowed the heavens, and came down: and darkness was under his feet.
10 Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
And he ascended upon the cherubim, and he flew; he flew upon the wings of the winds.
11 Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
And he made darkness his covert, his pavilion round about him: dark waters in the clouds of the air.
12 daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
At the brightness that was before him the clouds passed, hail and coals of fire.
13 Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
And the Lord thundered from heaven, and the highest gave his voice: hail and coals of fire.
14 Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
And he sent forth his arrows, and he scattered them: he multiplied lightnings, and troubled them.
15 Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
Then the fountains of waters appeared, and the foundations of the world were discovered: At thy rebuke, O Lord, at the blast of the spirit of thy wrath.
16 Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
He sent from on high, and took me: and received me out of many waters.
17 Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
He delivered me from my strongest enemies, and from them that hated me: for they were too strong for me.
18 Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
They prevented me in the day of my affliction: and the Lord became my protector.
19 Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
And he brought me forth into a large place: he saved me, because he was well pleased with me.
20 Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
And the Lord will reward me according to my justice; and will repay me according to the cleanness of my hands:
21 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
Because I have kept the ways of the Lord; and have not done wickedly against my God.
22 Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
For till his judgments are in my sight: and his justices I have not put away from me.
23 Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
And I shall be spotless with him: and shall keep myself from my iniquity.
24 Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
And the Lord will reward me according to my justice; and according to the cleanness of my hands before his eyes.
25 Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
With the holy, thou wilt be holy; and with the innocent man thou wilt be innocent.
26 ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
And with the elect thou wilt be elect: and with the perverse thou wilt be perverted.
27 Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
For thou wilt save the humble people; but wilt bring down the eyes of the proud.
28 Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
For thou lightest my lamp, O Lord: O my God enlighten my darkness.
29 Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
For by thee I shall be delivered from temptation; and through my God I shall go over a wall.
30 Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
As for my God, his way is undefiled: the words of the Lord are fire tried: he is the protector of all that trust in him.
31 Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
For who is God but the Lord? or who is God but our God?
32 Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
God who hath girt me with strength; and made my way blameless.
33 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
Who hath made my feet like the feet of harts: and who setteth me upon high places.
34 Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
Who teacheth my hands to war: and thou hast made my arms like a brazen bow.
35 Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
And thou hast given me the protection of thy salvation: and thy right hand hath held me up: And thy discipline hath corrected me unto the end: and thy discipline, the same shall teach me.
36 Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
Thou hast enlarged my steps under me; and my feet are not weakened.
37 Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
I will pursue after my enemies, and overtake them: and I will not turn again till they are consumed.
38 Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
I will break them, and they shall not be able to stand: they shall fall under my feet.
39 Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
And thou hast girded me with strength unto battle; and hast subdued under me them that rose up against me.
40 Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
And thou hast made my enemies turn their back upon me, and hast destroyed them that hated me.
41 Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
They cried, but there was none to save them, to the Lord: but he heard them not.
42 Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
And I shall beat them as small as the dust before the wind; I shall bring them to nought, like the dirt in the streets.
43 Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
Thou wilt deliver me from the contradictions of the people: thou wilt make me head of the Gentiles.
44 da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
A people, which I knew not, hath served me: at the hearing of the ear they have obeyed me.
45 Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
The children that are strangers have lied to me, strange children have faded away, and have halted from their paths.
46 Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
The Lord liveth, and blessed be my God, and let the God of my salvation be exalted:
47 Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
O God, who avengest me, and subduest the people under me, my deliverer from my enemies.
48 wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
And thou wilt lift me up above them that rise up against me: from the unjust man thou wilt deliver me.
49 Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
Therefore will I give glory to thee, O Lord, among the nations, and I will sing a psalm to thy name.
50 Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.
Giving great deliverance to his king, and shewing mercy to David his anointed: and to his seed for ever.