< Zabura 18 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
Učitelju zbora. Od Jahvina sluge Davida koji Jahvi ispjeva ovu pjesmu u onaj dan kad ga Jahve oslobodi iz ruku neprijatelja Ljubim te, Jahve, kreposti moja!
2 Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
Jahve, hridino moja, utvrdo moja spase moj; Bože moj, pećino moja kojoj se utječem, štite moj, snago spasenja moga, tvrđavo moja!
3 Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
Zazvat ću Jahvu, hvale predostojna, i od dušmana bit ću izbavljen.
4 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
Valovi smrti okružiše mene, prestraviše me bujice pogubne.
5 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol )
Užad Podzemlja sputiše me, smrtonosne zamke padoše na me: (Sheol )
6 Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
u nevolji zazvah Jahvu i Bogu svome zavapih. Iz svog Hrama zov mi začu, i vapaj moj mu do ušiju doprije.
7 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
I zemlja se potrese i uzdrhta, uzdrmaše se temelji gora, pokrenuše se, jer On gnjevom planu.
8 Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
Iz nosnica mu dim se diže, iz usta mu oganj liznu, ugljevlje živo od njega plamsa.
9 Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
On nagnu nebesa i siđe, pod nogama oblaci mu mračni.
10 Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
Na keruba stade i poletje; na krilima vjetra zaplovi.
11 Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
Ogrnu se mrakom kao koprenom, prekri se tamnim vodama i oblacima tmastim,
12 daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
od blijeska pred licem njegovim užga se ugljevlje plameno.
13 Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
Jahve s neba zagrmje, Svevišnjega glas se ori.
14 Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
Odape strijele i dušmane rasu, izbaci munje i na zemlju ih obori.
15 Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
Morska se dna pokazaše, i temelji svijeta postaše goli od strašne prijetnje Jahvine, od olujna daha gnjeva njegova.
16 Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
On pruži s neba ruku i mene prihvati, iz silnih voda on me izbavi.
17 Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
Od protivnika moćnog mene oslobodi, od dušmana mojih jačih od mene.
18 Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
Navališe na me u dan zlosretni, ali me Jahve zaštiti,
19 Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
na polje prostrano izvede me, spasi me jer sam mu mio.
20 Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
Po pravednosti mojoj Jahve mi uzvrati, po čistoći ruku mojih on me nagradi,
21 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
jer čuvah putove Jahvine, od Boga se svoga ne udaljih.
22 Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
Odredbe njegove sve su mi pred očima, zapovijedi njegove nisam odbacio,
23 Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
do srži odan njemu sam bio, čuvam se grijeha svakoga.
24 Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
Jahve mi po pravdi mojoj vrati, čistoću ruku mojih vidje.
25 Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
S prijateljem ti si prijatelj, poštenu poštenjem uzvraćaš.
26 ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
S čovjekom čistim ti si čist, a lukavca izigravaš,
27 Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
jer narodu poniženu spasenje donosiš, a ponižavaš oči ohole.
28 Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
Jahve, ti moju svjetiljku užižeš, Bože, tminu moju obasjavaš:
29 Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
s tobom udaram na čete dušmanske, s Bogom svojim preskačem zidine.
30 Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
Savršeni su puti Gospodnji, i riječ je Božja ognjem kušana. On, samo on, štit je svima koji se k njemu utječu.
31 Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
Jer tko je Bog osim Jahve? Tko li je hridina osim Boga našega?
32 Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
Taj Bog me snagom opasuje, stere mi put besprijekoran,
33 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
noge mi dade brze k'o u košute i postavi me na visine čvrste,
34 Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
ruke mi za borbu uvježba i mišice da luk mjedeni napinju.
35 Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
Daješ mi štit svoj koji spasava, tvoja me desnica drži, tvoja me brižljivost uzvisi.
36 Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
Pouzdanje daješ mom koraku, i noge mi više ne posrću.
37 Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
Pognah svoje dušmane i dostigoh, i ne vratih se dok ih ne uništih.
38 Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
Obaram ih, ne mogu se dići, padaju, pod nogama mi leže.
39 Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
Ti me opasa snagom za borbu, a protivnike moje meni podloži.
40 Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
Ti dušmane moje u bijeg natjera, i rasprših one koji su me mrzili.
41 Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
Vapiju u pomoć - nikog da pomogne; vapiju Jahvi - ne odaziva se.
42 Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
Smrvih ih kao prah na vjetru, zgazih ih k'o blato na putu.
43 Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
Ti me izbavi od bune u mom narodu, postavi me glavarom pogana, puk koji ne poznavah služi mi.
44 da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
Svaki moj šapat pokorno on sluša, sinovi tuđinci meni laskaju;
45 Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
sinovi tuđinski gube srčanost, izlaze dršćuć' iz svojih utvrda.
46 Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
Živio Jahve! Blagoslovljena hridina moja! Neka se uzvisi Bog, spasenje moje!
47 Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
Bog koji mi daje osvetu i narode meni pokorava.
48 wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
Od dušmana me mojih izbavljaš i nad protivnike me moje izdižeš, ti mene od čovjeka silnika spasavaš.
49 Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
Zato te slavim, Jahve, među pucima i psalam pjevam tvome Imenu:
50 Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.
umnožio si pobjede kralju svojemu, pomazaniku svome milost si iskazao, Davidu i potomstvu njegovu navijeke.