< Zabura 17 >
1 Addu’a ce ta Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.
Молитва Дави́дова.
2 Bari fiffitawata tă zo daga gare ka; bari idanunka su ga abin da yake daidai.
Від Твого лиця нехай вирок мій ви́йде, а очі Твої нехай бачать мою правоту́!
3 Ko ka duba zuciyata, ka kuma bincike ni da dare, ko ka gwada ni, ba za ka sami kome ba; na yanke shawara cewa bakina ba zai yi zunubi ba.
Ти ви́пробував моє серце, навісти́в уночі, перетопи́в Ти мене, — й не знайшов чогось злого. І розду́мував я, щоб лихе з моїх уст не вихо́дило,
4 Game da ayyukan mutane kuwa, ta wurin maganar leɓunanka na kiyaye kaina daga hanyoyin tashin hankali.
а в лю́дських діла́х, за словом уст Твоїх, я стерігся доріг гнобителя.
5 Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
Зміцняй сто́пи мої на доро́гах Твоїх, щоб кро́ки мої не хита́лися!
6 Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini; ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
Я кли́чу до Тебе, бо відповіси́ мені, Боже, — нахили Своє ухо до мене, вислухай мову мою,
7 Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki, kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu da hannunka na dama.
покажи дивну милість Свою, Спасителю тих, хто вдає́ться до Тебе від заколо́тників проти прави́ці Твоєї.
8 Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido; ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
Хорони Ти мене, як зіни́цю Свою, дочку ока, у тіні Своїх крил заховай Ти мене
9 daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
від безбожних, що гублять мене, — смертельні мої вороги оточили мене!
10 Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
То́вщем замкнули вони своє серце, уста їхні говорять бундю́чно.
11 Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
Вороги оточили тепер наші кро́ки, наставили очі свої, щоб мене повалити на землю.
12 Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
Із них кожен подібний до лева, що ша́рпати прагне, й як левчук, що сидить в укритті́.
13 Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
Устань же, о Господи, — його попере́дь, кинь його на коліна! Мечем Своїм душу мою збережи від безбожного,
14 Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so;’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa’ya’yansu.
від людей рукою Своєю, Господи, від людей цього світу, що частка їхня в цьому житті, що Ти скарбом Своїм наповня́єш їхнє че́рево! Ситі їхні сини, останок же свій для дітей вони ли́шать.
15 Amma ni, cikin adalci zan ga fuskarka; sa’ad da na farka, zan gamsu da ganin kamanninka.
А я в правді побачу обли́ччя Твоє, і, збудившись, наси́чусь Твоєю подо́бою!