< Zabura 17 >
1 Addu’a ce ta Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.
En bön av David. Hör, o HERRE, en rättfärdig sak, akta på mitt rop, lyssna till min bön; den kommer icke ifrån falska läppar.
2 Bari fiffitawata tă zo daga gare ka; bari idanunka su ga abin da yake daidai.
Av dig må jag få min rätt; dina ögon må skåda vad rättvist är.
3 Ko ka duba zuciyata, ka kuma bincike ni da dare, ko ka gwada ni, ba za ka sami kome ba; na yanke shawara cewa bakina ba zai yi zunubi ba.
Du prövar mitt hjärta, du utrannsakar mig, men du finner intet; ingen ond tanke går ut ur min mun.
4 Game da ayyukan mutane kuwa, ta wurin maganar leɓunanka na kiyaye kaina daga hanyoyin tashin hankali.
Efter dina läppars ord, och vad människor än må göra, tager jag mig till vara för våldsverkares stigar.
5 Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
Mina steg hålla sig stadigt på dina vägar, mina fötter vackla icke.
6 Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini; ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
Så åkallar jag nu dig, ty du, Gud, skall svara mig; böj ditt öra till mig, hör mitt tal.
7 Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki, kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu da hannunka na dama.
Bevisa din underbara nåd, du som frälsar undan motståndarna dem som taga sin tillflykt till din högra hand.
8 Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido; ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
Bevara mig såsom en ögonsten, beskärma mig under dina vingars skugga
9 daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
för de ogudaktiga, som vilja fördärva mig, för mina dödsfiender, som omringa mig.
10 Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
Sitt hjärta förstocka de; med sin mun tala de stora ord.
11 Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
Nu äro de omkring mig, var vi gå, deras ögon speja efter huru de skola böja mig till jorden.
12 Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
Ja, denne är lik ett lejon som längtar efter rov, lik ett ungt lejon som ligger i försåt.
13 Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
Stå upp, HERRE; träd emot honom, slå honom ned, rädda med ditt svärd min själ från den ogudaktige,
14 Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so;’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa’ya’yansu.
ja, med din hand, från människorna, HERRE, från denna världens människor, som hava sin del i detta livet, och vilkas buk du fyller med dina håvor, som hava söner i mängd och lämna sitt överflöd åt sina barn.
15 Amma ni, cikin adalci zan ga fuskarka; sa’ad da na farka, zan gamsu da ganin kamanninka.
Men jag skall skåda ditt ansikte i rättfärdighet; när jag uppvaknar, vill jag mätta mig av din åsyn.