< Zabura 17 >

1 Addu’a ce ta Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.
En bön Davids. Herre, hör rätthetena; gif akt uppå mitt rop, förnim mina bön, den icke utaf en falsk mun går.
2 Bari fiffitawata tă zo daga gare ka; bari idanunka su ga abin da yake daidai.
Tala du i mine sak, och se du uppå hvad rätt är.
3 Ko ka duba zuciyata, ka kuma bincike ni da dare, ko ka gwada ni, ba za ka sami kome ba; na yanke shawara cewa bakina ba zai yi zunubi ba.
Du pröfvar mitt hjerta, och besöker det om nattena, och ransakar mig, och finner intet; jag hafver satt mig före, att min mun icke öfverträda skall.
4 Game da ayyukan mutane kuwa, ta wurin maganar leɓunanka na kiyaye kaina daga hanyoyin tashin hankali.
Jag förvarar mig i dina läppars orde, för menniskors gerningar, på mördarens väg.
5 Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
Behåll min gång på dinom stigom, att min steg icke slinta.
6 Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini; ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
Jag ropar till dig, att du Gud ville höra, mig; böj din öron till mig, hör mitt tal.
7 Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki, kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu da hannunka na dama.
Bevisa, dina underliga godhet, du, deras Frälsare, som trösta uppå dig, emot dem som sig emot dina högra hand sätta.
8 Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido; ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
Bevara mig såsom en ögnasten; beskärma mig under dina vingars skugga;
9 daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
För de ogudaktiga, som mig förhärja; för mina ovänner, som efter mina själ stå allt omkring.
10 Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
Deras fete hålla tillsamman; de tala med sin mun stor ord.
11 Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
Hvar vi gå, så äro de kringom oss; sina ögon ställa de derefter, att de måga slå oss till jordena;
12 Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
Såsom ett lejon, som rof begärar; såsom ett ungt lejon, som i kulone sitter.
13 Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
Herre, statt upp, öfverfall honom, och nederslå honom; undsätt mina själ ifrå de ogudaktiga, med ditt svärd;
14 Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so;’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa’ya’yansu.
Ifrå dine hands menniskom, Herre, ifrå denne verldenes menniskom, hvilka sin del hafva medan de lefva; dem du buken fyller med dina håfvor; de der barn nog hafva, och låta sina återlefvor sinom barnom.
15 Amma ni, cikin adalci zan ga fuskarka; sa’ad da na farka, zan gamsu da ganin kamanninka.
Men jag vill skåda ditt ansigte i rättfärdighet; jag vill mätt varda, när jag uppvakar efter ditt beläte.

< Zabura 17 >