< Zabura 17 >

1 Addu’a ce ta Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.
Oración de David. Oye, oh SEÑOR, justicia; está atento a mi clamor; escucha mi oración hecha sin labios de engaño.
2 Bari fiffitawata tă zo daga gare ka; bari idanunka su ga abin da yake daidai.
De delante de tu rostro salga mi juicio; vean tus ojos la rectitud.
3 Ko ka duba zuciyata, ka kuma bincike ni da dare, ko ka gwada ni, ba za ka sami kome ba; na yanke shawara cewa bakina ba zai yi zunubi ba.
Tú has probado mi corazón, me has visitado de noche; me has refinado, y nada inicuo hallaste; lo que pensé, no pasó mi boca.
4 Game da ayyukan mutane kuwa, ta wurin maganar leɓunanka na kiyaye kaina daga hanyoyin tashin hankali.
Para las obras humanas, por la palabra de tus labios yo observé los caminos del violento.
5 Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
Sustenta mis pasos en tus caminos, para que mis pies no resbalen.
6 Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini; ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
Yo te he invocado, por cuanto tú me oyes, oh Dios: Inclina a mí tu oído, escucha mi palabra.
7 Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki, kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu da hannunka na dama.
Haz maravillosas tus misericordias, salvador de los que en ti confían, de los que se levantan contra tu diestra.
8 Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido; ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
Guárdame como lo negro de la niña del ojo, escóndeme con la sombra de tus alas.
9 daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
De delante de los malos que me oprimieron, de mis enemigos que me cercan por la vida.
10 Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
Cerrados están con su grosura; con su boca hablan soberbiamente.
11 Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
Nuestros pasos nos han cercado ahora; puestos tienen sus ojos para echarnos por tierra.
12 Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
Parecen al león que desea hacer presa, y al leoncillo que está escondido.
13 Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
Levántate, oh SEÑOR; prevén su encuentro, póstrale; libra mi alma del malo con tu espada;
14 Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so;’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa’ya’yansu.
de los hombres con tu mano, oh SEÑOR, de los hombres de mundo, cuya parte es en esta vida, y cuyo vientre está lleno de tu despensa: sacian a sus hijos, y dejan el resto a su familia.
15 Amma ni, cikin adalci zan ga fuskarka; sa’ad da na farka, zan gamsu da ganin kamanninka.
Yo en justicia veré tu rostro; seré saciado cuando despertaré a tu semejanza.

< Zabura 17 >