< Zabura 17 >
1 Addu’a ce ta Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.
Una oración de David. Escucha, Yahvé, mi justa súplica. Presta atención a mi oración que no sale de labios engañosos.
2 Bari fiffitawata tă zo daga gare ka; bari idanunka su ga abin da yake daidai.
Que mi sentencia salga de tu presencia. Deja que tus ojos miren la equidad.
3 Ko ka duba zuciyata, ka kuma bincike ni da dare, ko ka gwada ni, ba za ka sami kome ba; na yanke shawara cewa bakina ba zai yi zunubi ba.
Has probado mi corazón. Me has visitado en la noche. Me has probado y no has encontrado nada. He resuelto que mi boca no desobedezca.
4 Game da ayyukan mutane kuwa, ta wurin maganar leɓunanka na kiyaye kaina daga hanyoyin tashin hankali.
En cuanto a las obras de los hombres, por la palabra de tus labios, Me he alejado de los caminos de los violentos.
5 Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
Mis pasos se han mantenido firmes en tus caminos. Mis pies no han resbalado.
6 Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini; ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
Te he invocado, porque tú me responderás, Dios. Poner el oído en mí. Escucha mi discurso.
7 Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki, kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu da hannunka na dama.
Muestra tu maravillosa bondad amorosa, tú que salvas a los que se refugian por tu derecha de sus enemigos.
8 Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido; ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
Guárdame como la niña de tus ojos. Escóndeme bajo la sombra de tus alas,
9 daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
de los malvados que me oprimen, mis enemigos mortales, que me rodean.
10 Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
Cierran sus corazones insensibles. Con la boca hablan con orgullo.
11 Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
Ahora nos han rodeado en nuestros pasos. Pusieron sus ojos en arrojarnos a la tierra.
12 Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
Es como un león ávido de su presa, como si fuera un joven león que acecha en lugares secretos.
13 Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
Levántate, Yahvé, enfréntate a él. Échalo abajo. Libra mi alma de los malvados con tu espada,
14 Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so;’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa’ya’yansu.
de los hombres por tu mano, Yahvé, de los hombres del mundo, cuya porción está en esta vida. Llenas la barriga de tus seres queridos. Sus hijos tienen mucho, y acumulan riquezas para sus hijos.
15 Amma ni, cikin adalci zan ga fuskarka; sa’ad da na farka, zan gamsu da ganin kamanninka.
En cuanto a mí, veré tu rostro en la justicia. Me conformaré, cuando despierte, con ver tu forma.