< Zabura 17 >
1 Addu’a ce ta Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.
Молитва Давида. Услышь, Господи, правду, внемли воплю моему, прими мольбу из уст нелживых.
2 Bari fiffitawata tă zo daga gare ka; bari idanunka su ga abin da yake daidai.
От Твоего лица суд мне да изыдет; да воззрят очи Твои на правоту.
3 Ko ka duba zuciyata, ka kuma bincike ni da dare, ko ka gwada ni, ba za ka sami kome ba; na yanke shawara cewa bakina ba zai yi zunubi ba.
Ты испытал сердце мое, посетил меня ночью, искусил меня и ничего не нашел; от мыслей моих не отступают уста мои.
4 Game da ayyukan mutane kuwa, ta wurin maganar leɓunanka na kiyaye kaina daga hanyoyin tashin hankali.
В делах человеческих, по слову уст Твоих, я охранял себя от путей притеснителя.
5 Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
Утверди шаги мои на путях Твоих, да не колеблются стопы мои.
6 Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini; ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
К Тебе взываю я, ибо Ты услышишь меня, Боже; приклони ухо Твое ко мне, услышь слова мои.
7 Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki, kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu da hannunka na dama.
Яви дивную милость Твою, Спаситель уповающих на Тебя от противящихся деснице Твоей.
8 Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido; ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
Храни меня, как зеницу ока; в тени крыл Твоих укрой меня
9 daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
от лица нечестивых, нападающих на меня, - от врагов души моей, окружающих меня:
10 Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
они заключились в туке своем, надменно говорят устами своими.
11 Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
На всяком шагу нашем ныне окружают нас; они устремили глаза свои, чтобы низложить меня на землю;
12 Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
они подобны льву, жаждущему добычи, подобны скимну, сидящему в местах скрытных.
13 Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
Восстань, Господи, предупреди их, низложи их. Избавь душу мою от нечестивого мечом Твоим,
14 Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so;’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa’ya’yansu.
от людей - рукою Твоею, Господи, от людей мира, которых удел в этой жизни, которых чрево Ты наполняешь из сокровищниц Твоих; сыновья их сыты и оставят остаток детям своим.
15 Amma ni, cikin adalci zan ga fuskarka; sa’ad da na farka, zan gamsu da ganin kamanninka.
А я в правде буду взирать на лице Твое; пробудившись, буду насыщаться образом Твоим.