< Zabura 17 >
1 Addu’a ce ta Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.
oratio David exaudi Domine iustitiam meam intende deprecationem meam auribus percipe orationem meam non in labiis dolosis
2 Bari fiffitawata tă zo daga gare ka; bari idanunka su ga abin da yake daidai.
de vultu tuo iudicium meum prodeat oculi tui videant aequitates
3 Ko ka duba zuciyata, ka kuma bincike ni da dare, ko ka gwada ni, ba za ka sami kome ba; na yanke shawara cewa bakina ba zai yi zunubi ba.
probasti cor meum visitasti nocte igne me examinasti et non est inventa in me iniquitas
4 Game da ayyukan mutane kuwa, ta wurin maganar leɓunanka na kiyaye kaina daga hanyoyin tashin hankali.
ut non loquatur os meum opera hominum propter verba labiorum tuorum ego custodivi vias duras
5 Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
perfice gressus meos in semitis tuis ut non moveantur vestigia mea
6 Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini; ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
ego clamavi quoniam exaudisti me Deus inclina aurem tuam mihi et exaudi verba mea
7 Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki, kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu da hannunka na dama.
mirifica misericordias tuas qui salvos facis sperantes in te
8 Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido; ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
a resistentibus dexterae tuae custodi me ut pupillam oculi sub umbra alarum tuarum proteges me
9 daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
a facie impiorum qui me adflixerunt inimici mei animam meam circumdederunt super me;
10 Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
adipem suum concluserunt os eorum locutum est superbia
11 Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
proicientes me nunc circumdederunt me oculos suos statuerunt declinare in terram
12 Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
susceperunt me sicut leo paratus ad praedam et sicut catulus leonis habitans in abditis
13 Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
exsurge Domine praeveni eum et subplanta eum eripe animam meam ab impio frameam tuam
14 Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so;’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa’ya’yansu.
ab inimicis manus tuae Domine a paucis de terra divide eos in vita eorum de absconditis tuis adimpletus est venter eorum saturati sunt filiis et dimiserunt reliquias suas parvulis suis
15 Amma ni, cikin adalci zan ga fuskarka; sa’ad da na farka, zan gamsu da ganin kamanninka.
ego autem in iustitia apparebo conspectui tuo satiabor cum apparuerit gloria tua