< Zabura 17 >

1 Addu’a ce ta Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.
Oratio David. Exaudi Domine iustitiam meam: intende deprecationem meam. Auribus percipe orationem meam, non in labiis dolosis.
2 Bari fiffitawata tă zo daga gare ka; bari idanunka su ga abin da yake daidai.
De vultu tuo iudicium meum prodeat: oculi tui videant æquitates.
3 Ko ka duba zuciyata, ka kuma bincike ni da dare, ko ka gwada ni, ba za ka sami kome ba; na yanke shawara cewa bakina ba zai yi zunubi ba.
Probasti cor meum, et visitasti nocte: igne me examinasti, et non est inventa in me iniquitas.
4 Game da ayyukan mutane kuwa, ta wurin maganar leɓunanka na kiyaye kaina daga hanyoyin tashin hankali.
Ut non loquatur os meum opera hominum: propter verba labiorum tuorum ego custodivi vias duras.
5 Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
Perfice gressus meos in semitis tuis: ut non moveantur vestigia mea.
6 Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini; ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
Ego clamavi, quoniam exaudisti me Deus: inclina aurem tuam mihi, et exaudi verba mea.
7 Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki, kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu da hannunka na dama.
Mirifica misericordias tuas, qui salvos facis sperantes in te.
8 Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido; ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
A resistentibus dexteræ tuæ custodi me, ut pupillam oculi. Sub umbra alarum tuarum protege me:
9 daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
a facie impiorum qui me afflixerunt. Inimici mei animam meam circumdederunt,
10 Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
adipem suum concluserunt: os eorum locutum est superbiam.
11 Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
Proiicientes me nunc circumdederunt me: oculos suos statuerunt declinare in terram.
12 Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
Susceperunt me sicut leo paratus ad prædam: et sicut catulus leonis habitans in abditis.
13 Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
Exurge Domine, præveni eum, et supplanta eum: eripe animam meam ab impio, frameam tuam ab inimicis manus tuæ.
14 Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so;’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa’ya’yansu.
Domine a paucis de terra divide eos in vita eorum: de absconditis tuis adimpletus est venter eorum. Saturati sunt filiis: et dimiserunt reliquias suas parvulis suis.
15 Amma ni, cikin adalci zan ga fuskarka; sa’ad da na farka, zan gamsu da ganin kamanninka.
Ego autem in iustitia apparebo conspectui tuo: satiabor cum apparuerit gloria tua.

< Zabura 17 >