< Zabura 17 >

1 Addu’a ce ta Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.
תפלה לדוד שמעה יהוה צדק הקשיבה רנתי האזינה תפלתי בלא שפתי מרמה׃
2 Bari fiffitawata tă zo daga gare ka; bari idanunka su ga abin da yake daidai.
מלפניך משפטי יצא עיניך תחזינה מישרים׃
3 Ko ka duba zuciyata, ka kuma bincike ni da dare, ko ka gwada ni, ba za ka sami kome ba; na yanke shawara cewa bakina ba zai yi zunubi ba.
בחנת לבי פקדת לילה צרפתני בל תמצא זמתי בל יעבר פי׃
4 Game da ayyukan mutane kuwa, ta wurin maganar leɓunanka na kiyaye kaina daga hanyoyin tashin hankali.
לפעלות אדם בדבר שפתיך אני שמרתי ארחות פריץ׃
5 Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
תמך אשרי במעגלותיך בל נמוטו פעמי׃
6 Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini; ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
אני קראתיך כי תענני אל הט אזנך לי שמע אמרתי׃
7 Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki, kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu da hannunka na dama.
הפלה חסדיך מושיע חוסים ממתקוממים בימינך׃
8 Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido; ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
שמרני כאישון בת עין בצל כנפיך תסתירני׃
9 daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
מפני רשעים זו שדוני איבי בנפש יקיפו עלי׃
10 Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
חלבמו סגרו פימו דברו בגאות׃
11 Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
אשרינו עתה סבבוני עיניהם ישיתו לנטות בארץ׃
12 Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
דמינו כאריה יכסוף לטרוף וככפיר ישב במסתרים׃
13 Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
קומה יהוה קדמה פניו הכריעהו פלטה נפשי מרשע חרבך׃
14 Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so;’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa’ya’yansu.
ממתים ידך יהוה ממתים מחלד חלקם בחיים וצפינך תמלא בטנם ישבעו בנים והניחו יתרם לעולליהם׃
15 Amma ni, cikin adalci zan ga fuskarka; sa’ad da na farka, zan gamsu da ganin kamanninka.
אני בצדק אחזה פניך אשבעה בהקיץ תמונתך׃

< Zabura 17 >