< Zabura 17 >

1 Addu’a ce ta Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.
Prière de David. Éternel, écoute ma juste cause! Sois attentif à mon cri! Prête l'oreille à ma prière: elle sort de lèvres sans fraude!
2 Bari fiffitawata tă zo daga gare ka; bari idanunka su ga abin da yake daidai.
Que ta présence fasse éclater mon droit; Que tes yeux reconnaissent mon intégrité!
3 Ko ka duba zuciyata, ka kuma bincike ni da dare, ko ka gwada ni, ba za ka sami kome ba; na yanke shawara cewa bakina ba zai yi zunubi ba.
Tu as sondé mon coeur, tu m'as visité pendant la nuit; Tu m'as éprouvé, tu ne trouves rien; Ma parole ne va pas au-delà de ma pensée.
4 Game da ayyukan mutane kuwa, ta wurin maganar leɓunanka na kiyaye kaina daga hanyoyin tashin hankali.
J'ai vu les actions des hommes; Mais, pour obéir à la parole de ta bouche. Je me suis éloigné des voies de l'homme violent.
5 Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
Affermis mes pas dans tes sentiers, Afin que mes pieds ne chancellent point.
6 Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini; ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
Je t'invoque; car tu m'exauces, ô Dieu! Incline ton oreille vers moi; écoute ma prière!
7 Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki, kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu da hannunka na dama.
Fais-nous admirer tes bontés, Toi qui sauves ceux qui cherchent leur refuge Auprès de toi, contre leurs adversaires!
8 Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido; ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
Garde-moi comme la prunelle de l'oeil! Cache-moi à l'ombre de tes ailes,
9 daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
Loin de ces méchants qui m'oppriment, De mes ennemis acharnés qui m'enveloppent!
10 Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
Ils ferment leur coeur à la pitié; Leur bouche tient des discours hautains.
11 Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
A chaque pas, ils nous circonviennent; Ils nous épient pour nous terrasser.
12 Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
Ils ressemblent au lion avide de déchirer. Au lionceau qui se tient aux aguets dans son repaire.
13 Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
Lève-toi, ô Éternel! Marche à la rencontre du méchant; renverse-le! Que ton épée me délivre de lui!
14 Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so;’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa’ya’yansu.
Que ta main, ô Éternel, me délivre de ces hommes, Des hommes de ce siècle, Dont tout le bonheur est dans cette vie, Et dont le ventre est gorgé de tes biens: Leurs enfants ont tout à satiété, Et ils laissent encore leur superflu à leurs petits-enfants.
15 Amma ni, cikin adalci zan ga fuskarka; sa’ad da na farka, zan gamsu da ganin kamanninka.
Mais moi, grâce à ma droiture, je pourrai voir ta face. A mon réveil, je me rassasierai de ta vue.

< Zabura 17 >