< Zabura 17 >
1 Addu’a ce ta Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.
Prière de David. Écoute, ô Éternel, la justice; sois attentif à mon cri; prête l’oreille à ma prière, qui ne s’élève pas de lèvres trompeuses.
2 Bari fiffitawata tă zo daga gare ka; bari idanunka su ga abin da yake daidai.
Que mon droit sorte de ta présence, que tes yeux regardent à la droiture.
3 Ko ka duba zuciyata, ka kuma bincike ni da dare, ko ka gwada ni, ba za ka sami kome ba; na yanke shawara cewa bakina ba zai yi zunubi ba.
Tu as sondé mon cœur, tu [m’]as visité de nuit; tu m’as éprouvé au creuset, tu n’as rien trouvé; ma pensée ne va pas au-delà de ma parole.
4 Game da ayyukan mutane kuwa, ta wurin maganar leɓunanka na kiyaye kaina daga hanyoyin tashin hankali.
Quant aux actions de l’homme, par la parole de tes lèvres je me suis gardé des voies de l’homme violent.
5 Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
Quand tu soutiens mes pas dans tes sentiers, mes pieds ne chancellent point.
6 Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini; ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
Je t’ai invoqué, car tu m’exauceras, ô Dieu! Incline ton oreille vers moi, écoute mes paroles.
7 Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki, kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu da hannunka na dama.
Rends admirable ta bonté, toi qui, par ta droite, sauves de [leurs] adversaires ceux qui se confient [en toi].
8 Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido; ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
Garde-moi comme la prunelle de l’œil; cache-moi sous l’ombre de tes ailes,
9 daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
De devant ces méchants qui me dévastent, mes ardents ennemis qui m’entourent.
10 Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
Ils sont enfermés dans leur propre graisse; de leur bouche, ils parlent avec hauteur.
11 Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
À [chacun de] nos pas, maintenant ils nous environnent; ils fixent leurs yeux, se baissant jusqu’à terre:
12 Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
Il est semblable au lion avide de déchirer, et comme le lionceau qui se tient dans les lieux cachés.
13 Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
Lève-toi, Éternel! devance-le, renverse-le; délivre mon âme du méchant [par] ton épée,
14 Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so;’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa’ya’yansu.
[Délivre-moi] des hommes [par] ta main, ô Éternel! des hommes de ce monde, [qui ont] leur portion dans cette vie, et dont tu remplis le ventre de tes biens cachés; ils sont rassasiés de fils, et ils laissent le reste de leurs [biens] à leurs enfants.
15 Amma ni, cikin adalci zan ga fuskarka; sa’ad da na farka, zan gamsu da ganin kamanninka.
Moi, je verrai ta face en justice; quand je serai réveillé, je serai rassasié de ton image.