< Zabura 17 >

1 Addu’a ce ta Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.
A Prayer of David. Hear, O Jehovah, righteousness, attend my cry, Give ear [to] my prayer, without lips of deceit.
2 Bari fiffitawata tă zo daga gare ka; bari idanunka su ga abin da yake daidai.
From before thee my judgment doth go out; Thine eyes do see uprightly.
3 Ko ka duba zuciyata, ka kuma bincike ni da dare, ko ka gwada ni, ba za ka sami kome ba; na yanke shawara cewa bakina ba zai yi zunubi ba.
Thou hast proved my heart, Thou hast inspected by night, Thou hast tried me, Thou findest nothing; My thoughts pass not over my mouth.
4 Game da ayyukan mutane kuwa, ta wurin maganar leɓunanka na kiyaye kaina daga hanyoyin tashin hankali.
As to doings of man, Through a word of Thy lips I have observed The paths of a destroyer;
5 Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
To uphold my goings in Thy paths, My steps have not slidden.
6 Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini; ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
I — I called Thee, for Thou dost answer me, O God, incline Thine ear to me, hear my speech.
7 Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki, kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu da hannunka na dama.
Separate wonderfully Thy kindness, O Saviour of the confiding, By Thy right hand, from withstanders.
8 Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido; ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
Keep me as the apple, the daughter of the eye; In shadow of Thy wings thou dost hide me.
9 daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
From the face of the wicked who spoiled me. Mine enemies in soul go round against me.
10 Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
Their fat they have closed up, Their mouths have spoken with pride:
11 Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
'Our steps now have compassed [him];' Their eyes they set to turn aside in the land.
12 Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
His likeness as a lion desirous to tear, As a young lion dwelling in secret places.
13 Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
Arise, O Jehovah, go before his face, Cause him to bend. Deliver my soul from the wicked, Thy sword,
14 Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so;’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa’ya’yansu.
From men, Thy hand, O Jehovah, From men of the world, their portion [is] in life, And [with] Thy hidden things Thou fillest their belly, They are satisfied [with] sons; And have left their abundance to their sucklings.
15 Amma ni, cikin adalci zan ga fuskarka; sa’ad da na farka, zan gamsu da ganin kamanninka.
I — in righteousness, I see Thy face; I am satisfied, in awaking, [with] Thy form!

< Zabura 17 >