< Zabura 17 >
1 Addu’a ce ta Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.
The prayer of Dauid. Heare the right, O Lord, consider my crye: hearken vnto my prayer of lips vnfained.
2 Bari fiffitawata tă zo daga gare ka; bari idanunka su ga abin da yake daidai.
Let my sentence come forth from thy presence, and let thine eyes beholde equitie.
3 Ko ka duba zuciyata, ka kuma bincike ni da dare, ko ka gwada ni, ba za ka sami kome ba; na yanke shawara cewa bakina ba zai yi zunubi ba.
Thou hast prooued and visited mine heart in the night: thou hast tryed me, and foundest nothing: for I was purposed that my mouth should not offend.
4 Game da ayyukan mutane kuwa, ta wurin maganar leɓunanka na kiyaye kaina daga hanyoyin tashin hankali.
Concerning the workes of men, by the wordes of thy lips I kept mee from the paths of the cruell man.
5 Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
Stay my steps in thy paths, that my feete doe not slide.
6 Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini; ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
I haue called vpon thee: surely thou wilt heare me, O God: incline thine eare to me, and hearken vnto my wordes.
7 Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki, kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu da hannunka na dama.
Shewe thy marueilous mercies, thou that art the Sauiour of them that trust in thee, from such as resist thy right hand.
8 Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido; ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
Keepe me as the apple of the eye: hide me vnder the shadowe of thy wings,
9 daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
From the wicked that oppresse mee, from mine enemies, which compasse me round about for my soule.
10 Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
They are inclosed in their owne fat, and they haue spoken proudely with their mouth.
11 Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
They haue compassed vs now in our steps: they haue set their eyes to bring downe to the ground:
12 Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
Like as a lyon that is greedy of pray, and as it were a lyons whelp lurking in secret places.
13 Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
Vp Lord, disappoint him: cast him downe: deliuer my soule from the wicked with thy sworde,
14 Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so;’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa’ya’yansu.
From men by thine hand, O Lord, from men of the world, who haue their portion in this life, whose bellies thou fillest with thine hid treasure: their children haue ynough, and leaue the rest of their substance for their children.
15 Amma ni, cikin adalci zan ga fuskarka; sa’ad da na farka, zan gamsu da ganin kamanninka.
But I will beholde thy face in righteousnes, and when I awake, I shalbe satisfied with thine image.