< Zabura 16 >

1 Miktam ne na Dawuda. Ka kiyaye ni, ya Allah, gama a cikinka nake samun mafaka.
En gyllen sang av David. Bevar mig, Gud! for jeg tar min tilflukt til dig.
2 Na ce wa Ubangiji, “Kai ne shugabana; in ba tare da kai ba, ba ni da wani abu mai kyau.”
Jeg sier til Herren: Du er min Herre; jeg har intet gode utenfor dig -
3 Game da tsarkakan da suke cikin ƙasar kuwa, su ne masu ɗaukakar da dukan farin cikina ya dangana.
idet jeg holder mig til de hellige som er i landet, og de herlige i hvem jeg har all min lyst.
4 Baƙin ciki zai ƙaru wa waɗanda suke bin waɗansu alloli. Ba zan zuba musu hadayarsu ta jini ba ko in ambaci sunayensu da bakina.
Mange sorger skal de ha som kjøper sig andre; jeg vil ikke utgyde deres drikkoffere av blod og ikke ta deres navn på mine leber.
5 Ubangiji, ka ba ni rabona da kwaf ɗin na; ka kiyaye rabona,
Herren er min tilfalne del og mitt beger; du gjør min lodd herlig.
6 Iyakoki sun fāɗo mini a wurare masu daɗi; tabbatacce ina da gādo mai bansha’awa.
En lodd er tilfalt mig som er liflig, og en arv som behager mig.
7 Zan yabi Ubangiji, wanda yake ba ni shawara; ko da dare ma zuciyata kan koya mini.
Jeg vil love Herren, som gav mig råd; også om nettene minner mine nyrer mig om det.
8 Kullum nakan sa Ubangiji a gabana. Gama yana a hannun damana, ba zan jijjigu ba.
Jeg setter alltid Herren for mig; for han er ved min høire hånd, jeg skal ikke rokkes.
9 Saboda haka zuciyata tana murna harshena kuma yana farin ciki; jikina kuma zai zauna lafiya,
Derfor gleder mitt hjerte sig, og min ære fryder sig; også mitt kjød skal bo i trygghet.
10 domin ba za ka yashe ni a kabari ba, ba kuwa za ka bar Mai Tsarkinka yă ruɓa ba. (Sheol h7585)
For du skal ikke overlate min sjel til dødsriket, du skal ikke la din hellige se forråtnelse. (Sheol h7585)
11 Ka sanar da ni hanyar rai; za ka cika ni da farin ciki a gabanka, da madawwamin jin daɗi a hannun damarka.
Du skal kunngjøre mig livets vei; gledes fylde er for ditt åsyn, livsalighet ved din høire hånd evindelig.

< Zabura 16 >