< Zabura 16 >

1 Miktam ne na Dawuda. Ka kiyaye ni, ya Allah, gama a cikinka nake samun mafaka.
Poème de David. Garde-moi, ô Dieu; car je cherche en toi mon refuge.
2 Na ce wa Ubangiji, “Kai ne shugabana; in ba tare da kai ba, ba ni da wani abu mai kyau.”
J'ai dit à l'Éternel: «Tu es le Seigneur; Toi seul, tu es mon bien suprême!»
3 Game da tsarkakan da suke cikin ƙasar kuwa, su ne masu ɗaukakar da dukan farin cikina ya dangana.
Et j'ai dit aux saints qui sont dans le pays: «Vous êtes les nobles âmes en qui je prends tout mon plaisir.»
4 Baƙin ciki zai ƙaru wa waɗanda suke bin waɗansu alloli. Ba zan zuba musu hadayarsu ta jini ba ko in ambaci sunayensu da bakina.
Les douleurs se multiplient Pour ceux qui courent après d'autres dieux. Je n'offrirai pas leurs libations de sang, Et les noms qu'ils invoquent ne seront pas sur mes lèvres.
5 Ubangiji, ka ba ni rabona da kwaf ɗin na; ka kiyaye rabona,
L'Éternel est ma part et mon breuvage: C'est lui qui me garde mon lot.
6 Iyakoki sun fāɗo mini a wurare masu daɗi; tabbatacce ina da gādo mai bansha’awa.
Ma portion m'est échue dans des lieux agréables; Oui, j'ai un bel héritage!
7 Zan yabi Ubangiji, wanda yake ba ni shawara; ko da dare ma zuciyata kan koya mini.
Je bénirai l'Éternel, qui est mon conseiller: Mon coeur m'y invite, même pendant la nuit.
8 Kullum nakan sa Ubangiji a gabana. Gama yana a hannun damana, ba zan jijjigu ba.
J'ai l'Éternel constamment présent devant moi: Puisqu'il est à ma droite, je ne serai point ébranlé.
9 Saboda haka zuciyata tana murna harshena kuma yana farin ciki; jikina kuma zai zauna lafiya,
C'est pourquoi mon coeur se réjouit, Et mon âme tressaille de joie; Mon corps même reposera en toute sécurité.
10 domin ba za ka yashe ni a kabari ba, ba kuwa za ka bar Mai Tsarkinka yă ruɓa ba. (Sheol h7585)
Car tu n'abandonneras pas mon âme dans le Séjour des morts. Tu ne permettras pas que celui qui t'aime voie la corruption. (Sheol h7585)
11 Ka sanar da ni hanyar rai; za ka cika ni da farin ciki a gabanka, da madawwamin jin daɗi a hannun damarka.
Tu me feras connaître le chemin de la vie. L'âme est rassasiée de joie en ta présence; Il y a des délices à ta droite, pour toujours!

< Zabura 16 >