< Zabura 16 >

1 Miktam ne na Dawuda. Ka kiyaye ni, ya Allah, gama a cikinka nake samun mafaka.
Écrit de David. Garde-moi, Seigneur, car j'ai mis en toi mon espérance.
2 Na ce wa Ubangiji, “Kai ne shugabana; in ba tare da kai ba, ba ni da wani abu mai kyau.”
J'ai dit au Seigneur: Tu es mon Seigneur, et tu n'as nul besoin de mes biens.
3 Game da tsarkakan da suke cikin ƙasar kuwa, su ne masu ɗaukakar da dukan farin cikina ya dangana.
Quant aux saints qui sont sur la terre, il a fait éclater toutes ses volontés pour eux.
4 Baƙin ciki zai ƙaru wa waɗanda suke bin waɗansu alloli. Ba zan zuba musu hadayarsu ta jini ba ko in ambaci sunayensu da bakina.
Leurs infirmités se sont multipliées, et cependant ils ont couru rapidement; je ne rassemblerai plus leurs synagogues de sang; et de mes lèvres je ne mentionnerai pas leur nom.
5 Ubangiji, ka ba ni rabona da kwaf ɗin na; ka kiyaye rabona,
Le Seigneur est la part de mon héritage et de mon calice; c'est toi, Seigneur, qui me restitueras mon héritage.
6 Iyakoki sun fāɗo mini a wurare masu daɗi; tabbatacce ina da gādo mai bansha’awa.
Les cordeaux sont tombés pour moi aux meilleures places; car mon héritage est excellent.
7 Zan yabi Ubangiji, wanda yake ba ni shawara; ko da dare ma zuciyata kan koya mini.
Je bénirai le Seigneur, qui m'a donné l'intelligence; mes désirs aussi me pressaient vivement jusque dans la nuit même.
8 Kullum nakan sa Ubangiji a gabana. Gama yana a hannun damana, ba zan jijjigu ba.
Je n'ai cessé de voir devant moi le Seigneur; car il se tient à ma droite, pour que je ne sois pas ébranlé.
9 Saboda haka zuciyata tana murna harshena kuma yana farin ciki; jikina kuma zai zauna lafiya,
C'est pourquoi mon cœur s'est réjoui, ma langue a tressailli d'allégresse, et ma chair se reposera dans l'espérance:
10 domin ba za ka yashe ni a kabari ba, ba kuwa za ka bar Mai Tsarkinka yă ruɓa ba. (Sheol h7585)
Parce que tu ne laisseras pas mon âme aux enfers; tu ne permettras pas que ton Saint voie la corruption. (Sheol h7585)
11 Ka sanar da ni hanyar rai; za ka cika ni da farin ciki a gabanka, da madawwamin jin daɗi a hannun damarka.
Tu m'as fait connaître les voies de la vie; tu me rempliras de joie par ton aspect; des délices éternelles sont à ta droite.

< Zabura 16 >