< Zabura 15 >

1 Zabura ta Dawuda. Ubangiji, wa zai zauna cikin wuri mai tsarkinka? Wa zai zauna a kan tudunka mai tsarki?
Gospod, kdo bo prebival v tvojem šotorskem svetišču? Kdo bo prebival na tvoji sveti gori?
2 Sai wanda ba shi da laifi kuma yana yin abin da yake daidai, wanda yake faɗin gaskiya daga zuciyarsa
Kdor živi pošteno in dela pravično in v svojem srcu govori resnico.
3 ba ya kuwa ɓata sunan wani da harshensa, wanda ba ya yi wa maƙwabcinsa mugunta ba ya kuwa baza jita-jita a kan ɗan’uwansa,
Kdor ne opravlja s svojim jezikom niti ne dela zla svojemu bližnjemu niti ne sprejema graje zoper svojega bližnjega.
4 wanda yake ƙin mugun mutum amma yakan girmama masu tsoron Ubangiji, yakan cika alkawarinsa ko da ma ya zafe shi,
V čigar očeh je podla oseba zaničevana, toda počasti tiste, ki se bojijo Gospoda. Ki prisega v svojo lastno škodo in se ne premisli.
5 wanda yake ba da rance ba tare da ruwa ba kuma ba ya karɓan cin hanci don yă kā da marar laifi. Shi wanda yake yin waɗannan abubuwa ba zai taɓa jijjiguwa ba.
Kdor ne izdaja svojega denarja za obresti niti ne sprejema nagrade zoper nedolžnega. Kdor dela te stvari, nikoli ne bo omajan.

< Zabura 15 >