< Zabura 15 >

1 Zabura ta Dawuda. Ubangiji, wa zai zauna cikin wuri mai tsarkinka? Wa zai zauna a kan tudunka mai tsarki?
Господи, кто обитает в жилищи Твоем? Или кто вселится во святую гору Твою?
2 Sai wanda ba shi da laifi kuma yana yin abin da yake daidai, wanda yake faɗin gaskiya daga zuciyarsa
Ходяй непорочен и делаяй правду, глаголяй истину в сердцы своем:
3 ba ya kuwa ɓata sunan wani da harshensa, wanda ba ya yi wa maƙwabcinsa mugunta ba ya kuwa baza jita-jita a kan ɗan’uwansa,
иже не ульсти языком своим и не сотвори искреннему своему зла, и поношения не прият на ближния своя:
4 wanda yake ƙin mugun mutum amma yakan girmama masu tsoron Ubangiji, yakan cika alkawarinsa ko da ma ya zafe shi,
уничижен есть пред ним лукавнуяй, боящыяжеся Господа славит: кленыйся искреннему своему и не отметаяся:
5 wanda yake ba da rance ba tare da ruwa ba kuma ba ya karɓan cin hanci don yă kā da marar laifi. Shi wanda yake yin waɗannan abubuwa ba zai taɓa jijjiguwa ba.
сребра своего не даде в лихву и мзды на неповинных не прият. Творяй сия не подвижится во век.

< Zabura 15 >