< Zabura 15 >

1 Zabura ta Dawuda. Ubangiji, wa zai zauna cikin wuri mai tsarkinka? Wa zai zauna a kan tudunka mai tsarki?
Psalm Dawida. PANIE, kto będzie przebywał w twoim przybytku? Kto zamieszka na twojej świętej górze?
2 Sai wanda ba shi da laifi kuma yana yin abin da yake daidai, wanda yake faɗin gaskiya daga zuciyarsa
[Ten], kto postępuje nienagannie i czyni sprawiedliwość, a w swoim sercu mówi prawdę;
3 ba ya kuwa ɓata sunan wani da harshensa, wanda ba ya yi wa maƙwabcinsa mugunta ba ya kuwa baza jita-jita a kan ɗan’uwansa,
Kto nie obmawia swym językiem, nie wyrządza bliźniemu nic złego, nie znieważa bliźniego;
4 wanda yake ƙin mugun mutum amma yakan girmama masu tsoron Ubangiji, yakan cika alkawarinsa ko da ma ya zafe shi,
Ten, przed którego oczami bezbożny jest wzgardzony, a który szanuje [tych], co się boją PANA; kto, choć przysięga na własną niekorzyść, nie wycofuje się;
5 wanda yake ba da rance ba tare da ruwa ba kuma ba ya karɓan cin hanci don yă kā da marar laifi. Shi wanda yake yin waɗannan abubuwa ba zai taɓa jijjiguwa ba.
Kto swych pieniędzy nie pożycza na lichwę i nie daje się przekupić przeciwko niewinnemu. Kto tak postępuje, nigdy się nie zachwieje.

< Zabura 15 >