< Zabura 15 >
1 Zabura ta Dawuda. Ubangiji, wa zai zauna cikin wuri mai tsarkinka? Wa zai zauna a kan tudunka mai tsarki?
Psaume de David. Seigneur, qui habitera dans ton tabernacle? Qui reposera sur ta montagne sainte?
2 Sai wanda ba shi da laifi kuma yana yin abin da yake daidai, wanda yake faɗin gaskiya daga zuciyarsa
Celui qui marche dans l'innocence et qui opère la justice; qui dit la vérité en son cœur
3 ba ya kuwa ɓata sunan wani da harshensa, wanda ba ya yi wa maƙwabcinsa mugunta ba ya kuwa baza jita-jita a kan ɗan’uwansa,
Et dont la langue n'a jamais trompé; qui n'a point fait tort à son prochain, et n'a point cru à la diffamation contre ses proches.
4 wanda yake ƙin mugun mutum amma yakan girmama masu tsoron Ubangiji, yakan cika alkawarinsa ko da ma ya zafe shi,
Le méchant n'est rien à ses yeux; il honore ceux qui craignent le Seigneur; s'il fait un serment à son prochain, il ne le trompe pas.
5 wanda yake ba da rance ba tare da ruwa ba kuma ba ya karɓan cin hanci don yă kā da marar laifi. Shi wanda yake yin waɗannan abubuwa ba zai taɓa jijjiguwa ba.
Il n'a point prêté son argent à usure; il n'a point accepté de dons contre l'innocent. Celui qui fait ces choses ne sera point ébranlé dans l'éternité.