< Zabura 15 >

1 Zabura ta Dawuda. Ubangiji, wa zai zauna cikin wuri mai tsarkinka? Wa zai zauna a kan tudunka mai tsarki?
[A Psalm by David.] Jehovah, who shall dwell in your sanctuary? Who shall live on your holy mountain?
2 Sai wanda ba shi da laifi kuma yana yin abin da yake daidai, wanda yake faɗin gaskiya daga zuciyarsa
He who walks blamelessly and does what is right, and speaks truth in his heart.
3 ba ya kuwa ɓata sunan wani da harshensa, wanda ba ya yi wa maƙwabcinsa mugunta ba ya kuwa baza jita-jita a kan ɗan’uwansa,
He doesn't slander with his tongue, nor does evil to his friend, nor lifts up an insult against his neighbor.
4 wanda yake ƙin mugun mutum amma yakan girmama masu tsoron Ubangiji, yakan cika alkawarinsa ko da ma ya zafe shi,
In his eyes a vile man is despised, but he honors those who fear Jehovah. He keeps an oath even when it hurts, and doesn't change it.
5 wanda yake ba da rance ba tare da ruwa ba kuma ba ya karɓan cin hanci don yă kā da marar laifi. Shi wanda yake yin waɗannan abubuwa ba zai taɓa jijjiguwa ba.
He doesn't lend out his money for interest, nor take a bribe against the innocent. The one who does these things will never be upended.

< Zabura 15 >