< Zabura 15 >

1 Zabura ta Dawuda. Ubangiji, wa zai zauna cikin wuri mai tsarkinka? Wa zai zauna a kan tudunka mai tsarki?
A psalm of David. Lord, who shall dwell in thy tabernacle? or who shall rest in thy holy hill?
2 Sai wanda ba shi da laifi kuma yana yin abin da yake daidai, wanda yake faɗin gaskiya daga zuciyarsa
He that walketh without blemish, and worketh justice:
3 ba ya kuwa ɓata sunan wani da harshensa, wanda ba ya yi wa maƙwabcinsa mugunta ba ya kuwa baza jita-jita a kan ɗan’uwansa,
He that speaketh truth in his heart, who hath not used deceit in his tongue: Nor hath done evil to his neighbour: nor taken up a reproach against his neighbours.
4 wanda yake ƙin mugun mutum amma yakan girmama masu tsoron Ubangiji, yakan cika alkawarinsa ko da ma ya zafe shi,
In his sight the malignant is brought to nothing: but he glorifieth them that fear the Lord. He that sweareth to his neighbour, and deceiveth not;
5 wanda yake ba da rance ba tare da ruwa ba kuma ba ya karɓan cin hanci don yă kā da marar laifi. Shi wanda yake yin waɗannan abubuwa ba zai taɓa jijjiguwa ba.
He that hath not put out his money to usury, nor taken bribes against the innocent: He that doth these things shall not be moved for ever.

< Zabura 15 >