< Zabura 15 >

1 Zabura ta Dawuda. Ubangiji, wa zai zauna cikin wuri mai tsarkinka? Wa zai zauna a kan tudunka mai tsarki?
A Psalm of David. O Lord, who shall sojourn in your tabernacle? and who shall dwell in your holy mountain?
2 Sai wanda ba shi da laifi kuma yana yin abin da yake daidai, wanda yake faɗin gaskiya daga zuciyarsa
He that walks blameless, and works righteousness, who speaks truth in his heart.
3 ba ya kuwa ɓata sunan wani da harshensa, wanda ba ya yi wa maƙwabcinsa mugunta ba ya kuwa baza jita-jita a kan ɗan’uwansa,
Who has not spoken craftily with is tongue, neither has done evil to his neighbour, nor taken up a reproach against them that lived nearest to him.
4 wanda yake ƙin mugun mutum amma yakan girmama masu tsoron Ubangiji, yakan cika alkawarinsa ko da ma ya zafe shi,
In his sight an evil-worker is set at nothing, but he honours them that fear the Lord. He swears to his neighbour, and disappoints [him] not.
5 wanda yake ba da rance ba tare da ruwa ba kuma ba ya karɓan cin hanci don yă kā da marar laifi. Shi wanda yake yin waɗannan abubuwa ba zai taɓa jijjiguwa ba.
He has not lent his money on usury, and has not received bribes against the innocent. He that does these things shall never be moved.

< Zabura 15 >