< Zabura 15 >

1 Zabura ta Dawuda. Ubangiji, wa zai zauna cikin wuri mai tsarkinka? Wa zai zauna a kan tudunka mai tsarki?
Jehovah, who shall sojourn in thy tabernacle? Who shall dwell in thy holy hill?
2 Sai wanda ba shi da laifi kuma yana yin abin da yake daidai, wanda yake faɗin gaskiya daga zuciyarsa
He who walks uprightly, and works righteousness, and speaks truth in his heart,
3 ba ya kuwa ɓata sunan wani da harshensa, wanda ba ya yi wa maƙwabcinsa mugunta ba ya kuwa baza jita-jita a kan ɗan’uwansa,
he who does no slander with his tongue, nor does evil to his friend, nor takes up a reproach against his neighbor,
4 wanda yake ƙin mugun mutum amma yakan girmama masu tsoron Ubangiji, yakan cika alkawarinsa ko da ma ya zafe shi,
in whose eyes a reprobate is despised, but who honors those who fear Jehovah, he that swears to his own hurt, and changes not,
5 wanda yake ba da rance ba tare da ruwa ba kuma ba ya karɓan cin hanci don yă kā da marar laifi. Shi wanda yake yin waɗannan abubuwa ba zai taɓa jijjiguwa ba.
he who puts not his money out to interest, nor takes a bribe against the innocent. He who does these things shall never be moved.

< Zabura 15 >