< Zabura 149 >
1 Yabi Ubangiji. Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji, yabonsa a cikin taron tsarkaka.
Hvalite Gospoda. Zapojte Gospodu novo pesem in njegovo hvalo v skupnosti svetih.
2 Bari Isra’ila su yi farin ciki da Mahaliccinsu; bari mutanen Sihiyona su yi murna da Sarkinsu.
Naj se Izrael veseli v njem, ki ga je naredil, naj bodo sionski otroci radostni v svojem Kralju.
3 Bari su yabi sunansa tare da rawa suna kuma yin kiɗi gare shi da ganga da garaya.
Naj s plesom hvalijo njegovo ime; naj mu prepevajo hvalnice s tamburinom in harfo.
4 Gama Ubangiji yana jin daɗin mutanensa; yakan darjanta masu sauƙinkai da ceto.
Kajti Gospod se veseli v svojem ljudstvu; krotke bo okrasil z rešitvijo duše.
5 Bari tsarkaka su yi farin ciki a wannan bangirma su kuma rera don farin ciki a kan gadajensu.
Naj bodo sveti radostni v slavi, naj na glas prepevajo na svojih posteljah.
6 Bari yabon Allah yă kasance a bakunansu takobi mai kaifi kuma a hannuwansu,
Naj bodo na njihovih ustih visoke Božje hvalnice in v njihovi roki dvorezen meč,
7 don su ɗau fansa a kan al’ummai da kuma hukunci a kan mutane,
da izvršijo maščevanje nad pogani in kaznovanja nad ljudstvi,
8 don su ɗaura sarakuna da sarƙoƙi, manyan garinsu da sarƙoƙin ƙarfe,
da njihove kralje zvežejo z verigami in njihove plemiče z železnimi okovi,
9 don su yi hukuncin da aka rubuta a kansu. Wannan ne ɗaukakar dukan tsarkakansa. Yabi Ubangiji.
da nad njimi izvršijo napisano sodbo. To čast imajo vsi sveti. Hvalite Gospoda.