< Zabura 149 >

1 Yabi Ubangiji. Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji, yabonsa a cikin taron tsarkaka.
ALLELUIA. Cantate al Signore un nuovo cantico; [Cantate] la sua lode nella raunanza de' santi.
2 Bari Isra’ila su yi farin ciki da Mahaliccinsu; bari mutanen Sihiyona su yi murna da Sarkinsu.
Rallegrisi Israele nel suo Fattore; Festiggino i figliuoli di Sion nel Re loro.
3 Bari su yabi sunansa tare da rawa suna kuma yin kiɗi gare shi da ganga da garaya.
Lodino il suo Nome sul flauto; Salmeggingli col tamburo e colla cetera.
4 Gama Ubangiji yana jin daɗin mutanensa; yakan darjanta masu sauƙinkai da ceto.
Perciocchè il Signore gradisce il suo popolo; Egli glorificherà i mansueti per la [sua] salute.
5 Bari tsarkaka su yi farin ciki a wannan bangirma su kuma rera don farin ciki a kan gadajensu.
I santi festeggeranno con gloria, Canteranno sopra i lor letti;
6 Bari yabon Allah yă kasance a bakunansu takobi mai kaifi kuma a hannuwansu,
Avranno nella lor gola le esaltazioni di Dio, E nelle mani spade a due tagli;
7 don su ɗau fansa a kan al’ummai da kuma hukunci a kan mutane,
Per far vendetta fra le genti, [E] castigamenti fra i popoli.
8 don su ɗaura sarakuna da sarƙoƙi, manyan garinsu da sarƙoƙin ƙarfe,
Per legare i loro re con catene, E gli onorati d'infra loro con ceppi di ferro;
9 don su yi hukuncin da aka rubuta a kansu. Wannan ne ɗaukakar dukan tsarkakansa. Yabi Ubangiji.
Per mandare ad esecuzione sopra loro il giudicio scritto; Il che [sarà] gloria a tutti i suoi santi. Alleluia.

< Zabura 149 >