< Zabura 148 >

1 Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji daga sammai, yabe shi a bisa sammai.
Lodate il Signore dai cieli, lodatelo nell'alto dei cieli. Alleluia.
2 Yabe shi, dukanku mala’ikunsa, yabe shi, dukanku rundunarsa na sama.
Lodatelo, voi tutti, suoi angeli, lodatelo, voi tutte, sue schiere.
3 Yabe shi, rana da wata, yabe shi, dukanku taurari masu haskakawa.
Lodatelo, sole e luna, lodatelo, voi tutte, fulgide stelle.
4 Yabe shi, ku bisa sammai da kuma ku ruwan bisa sarari.
Lodatelo, cieli dei cieli, voi acque al di sopra dei cieli.
5 Bari su yabi sunan Ubangiji, gama ya umarta aka kuwa halicce su.
Lodino tutti il nome del Signore, perché egli disse e furono creati.
6 Ya sa su a wurarensu har abada abadin; ya ba da umarnin da ba zai taɓa shuɗe ba.
Li ha stabiliti per sempre, ha posto una legge che non passa.
7 Yabi Ubangiji daga duniya, ku manyan halittun teku da kuma dukan zurfafan teku,
Lodate il Signore dalla terra, mostri marini e voi tutti abissi,
8 walƙiya da ƙanƙara, dusar ƙanƙara da gizagizai, hadirin iskar da suke biyayya da umarnansa,
fuoco e grandine, neve e nebbia, vento di bufera che obbedisce alla sua parola,
9 ku duwatsu da dukan tuddai, itatuwa masu’ya’ya da dukan al’ul,
monti e voi tutte, colline, alberi da frutto e tutti voi, cedri,
10 namun jeji da dukan dabbobin gida, ƙanana halittu da tsuntsaye masu firiya,
voi fiere e tutte le bestie, rettili e uccelli alati.
11 sarakunan duniya da dukan al’ummai, ku sarakuna da dukan masu mulkin duniya,
I re della terra e i popoli tutti, i governanti e i giudici della terra,
12 samari da’yan mata, tsofaffi da yara.
i giovani e le fanciulle, i vecchi insieme ai bambini
13 Bari su yabi sunan Ubangiji, gama sunansa ne kaɗai mafi ɗaukaka; darajarsa ta fi ƙarfin duniya da sammai.
lodino il nome del Signore: perché solo il suo nome è sublime, la sua gloria risplende sulla terra e nei cieli.
14 Ya tayar wa mutanensa ƙaho, yabon dukan tsarkakansa, na Isra’ila, mutanen da suke kurkusa da zuciyarsa. Yabi Ubangiji.
Egli ha sollevato la potenza del suo popolo. E' canto di lode per tutti i suoi fedeli, per i figli di Israele, popolo che egli ama. Alleluia.

< Zabura 148 >