< Zabura 148 >
1 Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji daga sammai, yabe shi a bisa sammai.
Hallelujah, lobet Jehovah von den Himmeln her, lobet Ihn in den Höhen!
2 Yabe shi, dukanku mala’ikunsa, yabe shi, dukanku rundunarsa na sama.
Lobet Ihn, alle Seine Engel! Lobet Ihn alle Seine Heerscharen!
3 Yabe shi, rana da wata, yabe shi, dukanku taurari masu haskakawa.
Lobet Ihn, Sonne und Mond, lobet Ihn, all ihr Sterne des Lichtes.
4 Yabe shi, ku bisa sammai da kuma ku ruwan bisa sarari.
Lobet Ihn, ihr Himmel der Himmel, und ihr Wasser, die ihr über den Himmeln seid!
5 Bari su yabi sunan Ubangiji, gama ya umarta aka kuwa halicce su.
Sie sollen den Namen Jehovahs loben; denn Er gebot, und sie waren geschaffen.
6 Ya sa su a wurarensu har abada abadin; ya ba da umarnin da ba zai taɓa shuɗe ba.
Und Er läßt sie stehen immerfort und in Ewigkeit, eine Satzung hat Er gegeben, und sie geht nicht vorüber.
7 Yabi Ubangiji daga duniya, ku manyan halittun teku da kuma dukan zurfafan teku,
Lobet Jehovah von der Erde, Walfische und alle Abgründe!
8 walƙiya da ƙanƙara, dusar ƙanƙara da gizagizai, hadirin iskar da suke biyayya da umarnansa,
Feuer und Hagel, Schnee und Dampf, Wind des Sturmes, der Sein Wort tut.
9 ku duwatsu da dukan tuddai, itatuwa masu’ya’ya da dukan al’ul,
Berge und Hügel alle, Fruchtbäume und alle Zedern!
10 namun jeji da dukan dabbobin gida, ƙanana halittu da tsuntsaye masu firiya,
Wild und alles Vieh, Kriechtiere und befiederte Vögel!
11 sarakunan duniya da dukan al’ummai, ku sarakuna da dukan masu mulkin duniya,
Könige der Erde und alle Volksstämme, ihr Obersten und alle Richter der Erde!
12 samari da’yan mata, tsofaffi da yara.
Jünglinge und auch Jungfrauen, Alte mit den Jungen.
13 Bari su yabi sunan Ubangiji, gama sunansa ne kaɗai mafi ɗaukaka; darajarsa ta fi ƙarfin duniya da sammai.
Jehovahs Namen sollen sie loben; denn hoch ist Sein Name allein, Seine Majestät über Erde und Himmel.
14 Ya tayar wa mutanensa ƙaho, yabon dukan tsarkakansa, na Isra’ila, mutanen da suke kurkusa da zuciyarsa. Yabi Ubangiji.
Und erhöht hat Er das Horn Seinem Volke, das Lob all Seinen Heiligen, den Söhnen Israel, dem Volke, das Ihm nahe ist. Hallelujah.