< Zabura 148 >

1 Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji daga sammai, yabe shi a bisa sammai.
Halleluja! Lobet den HERRN vom Himmel her, lobet ihn in den Himmelshöhen!
2 Yabe shi, dukanku mala’ikunsa, yabe shi, dukanku rundunarsa na sama.
Lobet ihn, alle seine Engel, lobet ihn, alle seine Heerscharen!
3 Yabe shi, rana da wata, yabe shi, dukanku taurari masu haskakawa.
Lobet ihn, Sonne und Mond, lobet ihn, alle ihr leuchtenden Sterne!
4 Yabe shi, ku bisa sammai da kuma ku ruwan bisa sarari.
Lobet ihn, ihr Himmel der Himmel, und ihr Wasser oberhalb des Himmels!
5 Bari su yabi sunan Ubangiji, gama ya umarta aka kuwa halicce su.
Loben sollen sie den Namen des HERRN, denn er gebot, da waren sie geschaffen,
6 Ya sa su a wurarensu har abada abadin; ya ba da umarnin da ba zai taɓa shuɗe ba.
und er hat sie hingestellt für immer und ewig und ihnen ein Gesetz gegeben, das übertreten sie nicht.
7 Yabi Ubangiji daga duniya, ku manyan halittun teku da kuma dukan zurfafan teku,
Lobet den HERRN von der Erde her, ihr Seeungeheuer und alle Meeresfluten,
8 walƙiya da ƙanƙara, dusar ƙanƙara da gizagizai, hadirin iskar da suke biyayya da umarnansa,
du Feuer und Hagel, du Schnee und Nebel, du Sturmwind, der sein Gebot vollzieht;
9 ku duwatsu da dukan tuddai, itatuwa masu’ya’ya da dukan al’ul,
ihr Berge und Hügel allesamt, ihr Fruchtbäume und Zedern allzumal,
10 namun jeji da dukan dabbobin gida, ƙanana halittu da tsuntsaye masu firiya,
ihr Tiere alle, wilde und zahme, du Gewürm und ihr beschwingte Vögel,
11 sarakunan duniya da dukan al’ummai, ku sarakuna da dukan masu mulkin duniya,
ihr Könige der Erde und alle Völkerschaften, ihr Fürsten und alle Richter auf Erden,
12 samari da’yan mata, tsofaffi da yara.
ihr Jünglinge mitsamt den Jungfrauen, ihr Greise samt den Jungen!
13 Bari su yabi sunan Ubangiji, gama sunansa ne kaɗai mafi ɗaukaka; darajarsa ta fi ƙarfin duniya da sammai.
Sie alle sollen loben den Namen des HERRN, denn sein Name allein ist erhaben; seine Hoheit überragt die Erde und den Himmel.
14 Ya tayar wa mutanensa ƙaho, yabon dukan tsarkakansa, na Isra’ila, mutanen da suke kurkusa da zuciyarsa. Yabi Ubangiji.
Er hat sein Volk aufs neue zu Ehren gebracht: ein Ruhm ist das für alle seine Frommen, für Israels Söhne, das Volk, das am nächsten ihm steht. Halleluja!

< Zabura 148 >