< Zabura 148 >
1 Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji daga sammai, yabe shi a bisa sammai.
Louez Yah! Louez Yahvé du haut des cieux! Louez-le dans les hauteurs!
2 Yabe shi, dukanku mala’ikunsa, yabe shi, dukanku rundunarsa na sama.
Louez-le, tous ses anges! Louez-le, toute son armée!
3 Yabe shi, rana da wata, yabe shi, dukanku taurari masu haskakawa.
Louez-le, soleil et lune! Louez-le, vous toutes, étoiles brillantes!
4 Yabe shi, ku bisa sammai da kuma ku ruwan bisa sarari.
Louez-le, cieux des cieux, vous les eaux qui sont au-dessus des cieux.
5 Bari su yabi sunan Ubangiji, gama ya umarta aka kuwa halicce su.
Qu'ils louent le nom de Yahvé, car il a ordonné, et ils ont été créés.
6 Ya sa su a wurarensu har abada abadin; ya ba da umarnin da ba zai taɓa shuɗe ba.
Il les a aussi établis pour toujours et à jamais. Il a pris un décret qui ne passera pas.
7 Yabi Ubangiji daga duniya, ku manyan halittun teku da kuma dukan zurfafan teku,
Louez Yahvé de toute la terre, vous les grandes créatures marines, et toutes les profondeurs,
8 walƙiya da ƙanƙara, dusar ƙanƙara da gizagizai, hadirin iskar da suke biyayya da umarnansa,
éclairs et grêle, neige et nuages, un vent de tempête, accomplissant sa parole,
9 ku duwatsu da dukan tuddai, itatuwa masu’ya’ya da dukan al’ul,
montagnes et toutes les collines, des arbres fruitiers et tous les cèdres,
10 namun jeji da dukan dabbobin gida, ƙanana halittu da tsuntsaye masu firiya,
animaux sauvages et tout le bétail, les petites créatures et les oiseaux volants,
11 sarakunan duniya da dukan al’ummai, ku sarakuna da dukan masu mulkin duniya,
les rois de la terre et tous les peuples, les princes et tous les juges de la terre,
12 samari da’yan mata, tsofaffi da yara.
tant les jeunes hommes que les jeunes filles, des vieillards et des enfants.
13 Bari su yabi sunan Ubangiji, gama sunansa ne kaɗai mafi ɗaukaka; darajarsa ta fi ƙarfin duniya da sammai.
Qu'ils louent le nom de Yahvé, car son nom seul est exalté. Sa gloire est au-dessus de la terre et des cieux.
14 Ya tayar wa mutanensa ƙaho, yabon dukan tsarkakansa, na Isra’ila, mutanen da suke kurkusa da zuciyarsa. Yabi Ubangiji.
Il a élevé la corne de son peuple, la louange de tous ses saints, même des enfants d'Israël, un peuple qui lui est proche. Louez Yah!