< Zabura 148 >
1 Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji daga sammai, yabe shi a bisa sammai.
Praise the Lord! Praise the Lord from heaven; praise him in the heights above!
2 Yabe shi, dukanku mala’ikunsa, yabe shi, dukanku rundunarsa na sama.
Praise him, all his angels; praise him, all his heavenly armies!
3 Yabe shi, rana da wata, yabe shi, dukanku taurari masu haskakawa.
Praise him, sun and moon! Praise him, all you shining stars!
4 Yabe shi, ku bisa sammai da kuma ku ruwan bisa sarari.
Praise him, highest heavens, and the waters above the heavens!
5 Bari su yabi sunan Ubangiji, gama ya umarta aka kuwa halicce su.
Let them all praise the Lord and his nature, for he gave the order and they were created.
6 Ya sa su a wurarensu har abada abadin; ya ba da umarnin da ba zai taɓa shuɗe ba.
He placed them in their positions forever and ever; he established a law that will never end.
7 Yabi Ubangiji daga duniya, ku manyan halittun teku da kuma dukan zurfafan teku,
Praise the Lord from the earth, and creatures from all the depths of the seas,
8 walƙiya da ƙanƙara, dusar ƙanƙara da gizagizai, hadirin iskar da suke biyayya da umarnansa,
lightning and hail, snow and clouds, and stormy wind—everything that does as he commands.
9 ku duwatsu da dukan tuddai, itatuwa masu’ya’ya da dukan al’ul,
Mountains and all the hills, fruit trees and all the trees of the forest,
10 namun jeji da dukan dabbobin gida, ƙanana halittu da tsuntsaye masu firiya,
wild animals and all livestock, crawling animals and wild birds,
11 sarakunan duniya da dukan al’ummai, ku sarakuna da dukan masu mulkin duniya,
earthly kings and all peoples, leaders and rulers of the world,
12 samari da’yan mata, tsofaffi da yara.
young men and women, old people and children—
13 Bari su yabi sunan Ubangiji, gama sunansa ne kaɗai mafi ɗaukaka; darajarsa ta fi ƙarfin duniya da sammai.
Let them all praise the Lord, for his reputation is unequalled; his glory is above anything on earth or in heaven.
14 Ya tayar wa mutanensa ƙaho, yabon dukan tsarkakansa, na Isra’ila, mutanen da suke kurkusa da zuciyarsa. Yabi Ubangiji.
He has given his people a source of strength, bringing praise to his faithful followers, the people of Israel who are dear to him. Praise the Lord!