< Zabura 148 >

1 Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji daga sammai, yabe shi a bisa sammai.
Give praise to the Lord. Let the Lord be praised from the heavens: give him praise in the skies.
2 Yabe shi, dukanku mala’ikunsa, yabe shi, dukanku rundunarsa na sama.
Give praise to him, all you his angels: give praise to him, all his armies.
3 Yabe shi, rana da wata, yabe shi, dukanku taurari masu haskakawa.
Give praise to him, you sun and moon: give praise to him, all you stars of light.
4 Yabe shi, ku bisa sammai da kuma ku ruwan bisa sarari.
Give praise to him, you highest heavens, and you waters which are over the heavens.
5 Bari su yabi sunan Ubangiji, gama ya umarta aka kuwa halicce su.
Let them give praise to the name of the Lord: for he gave the order, and they were made.
6 Ya sa su a wurarensu har abada abadin; ya ba da umarnin da ba zai taɓa shuɗe ba.
He has put them in their places for ever; he has given them their limits which may not be broken.
7 Yabi Ubangiji daga duniya, ku manyan halittun teku da kuma dukan zurfafan teku,
Give praise to the Lord from the earth, you great sea-beasts, and deep places:
8 walƙiya da ƙanƙara, dusar ƙanƙara da gizagizai, hadirin iskar da suke biyayya da umarnansa,
Fire and rain of ice, snow and mists; storm-wind, doing his word:
9 ku duwatsu da dukan tuddai, itatuwa masu’ya’ya da dukan al’ul,
Mountains and all hills; fruit-trees and all trees of the mountains:
10 namun jeji da dukan dabbobin gida, ƙanana halittu da tsuntsaye masu firiya,
Beasts and all cattle; insects and winged birds:
11 sarakunan duniya da dukan al’ummai, ku sarakuna da dukan masu mulkin duniya,
Kings of the earth, and all peoples; rulers and all judges of the earth:
12 samari da’yan mata, tsofaffi da yara.
Young men and virgins; old men and children:
13 Bari su yabi sunan Ubangiji, gama sunansa ne kaɗai mafi ɗaukaka; darajarsa ta fi ƙarfin duniya da sammai.
Let them give glory to the name of the Lord: for his name only is to be praised: his kingdom is over the earth and the heaven.
14 Ya tayar wa mutanensa ƙaho, yabon dukan tsarkakansa, na Isra’ila, mutanen da suke kurkusa da zuciyarsa. Yabi Ubangiji.
He has put on high the horn of his people, for the praise of all his saints; even the children of Israel, a people which is near to him. Let the Lord be praised.

< Zabura 148 >