< Zabura 147 >

1 Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
Alabado sea Yah, porque es bueno cantar alabanzas a nuestro Dios; porque es agradable y conveniente alabarlo.
2 Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
Yahvé construye Jerusalén. Reúne a los parias de Israel.
3 Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
Él cura a los quebrantados de corazón, y venda sus heridas.
4 Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
Cuenta el número de las estrellas. Los llama a todos por su nombre.
5 Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
Grande es nuestro Señor, y poderoso en poder. Su comprensión es infinita.
6 Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
Yahvé sostiene a los humildes. Derriba a los malvados al suelo.
7 Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
Canten a Yahvé con acción de gracias. Canta alabanzas con el arpa a nuestro Dios,
8 Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
que cubre el cielo de nubes, que prepara la lluvia para la tierra, que hace crecer la hierba en las montañas.
9 Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
Proporciona alimento para el ganado, y para los jóvenes cuervos cuando llaman.
10 Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
No se deleita en la fuerza del caballo. No se complace en las piernas de un hombre.
11 Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
Yahvé se complace en los que le temen, en los que esperan en su amorosa bondad.
12 Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
¡Alabado sea Yahvé, Jerusalén! ¡Alabado sea tu Dios, Sión!
13 Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
Porque ha reforzado los barrotes de tus puertas. Él ha bendecido a tus hijos dentro de ti.
14 Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
Él hace la paz en tus fronteras. Te llena de lo mejor del trigo.
15 Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
Él envía su mandamiento a la tierra. Su palabra corre muy rápido.
16 Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
Él da la nieve como la lana, y dispersa la escarcha como las cenizas.
17 Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
Arroja su granizo como si fueran guijarros. ¿Quién puede enfrentarse a su frío?
18 Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
Envía su palabra y los derrite. Él hace soplar su viento, y las aguas fluyen.
19 Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
Muestra su palabra a Jacob, sus estatutos y sus ordenanzas a Israel.
20 Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.
No lo ha hecho por cualquier nación. No conocen sus ordenanzas. ¡Alabado sea Yah!

< Zabura 147 >