< Zabura 147 >

1 Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
¡Alaben al Señor, porque es bueno cantar alabanzas a Dios! ¡Alabarle es bueno y maravilloso!
2 Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
El Señor reconstruirá Jerusalén y reunirá al pueblo que ha sido esparcido.
3 Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
Él sana a los de corazón quebrantado, y venda las heridas.
4 Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
Él sabe cuántas estrellas fueron hechas, y las llama a cada una por su nombre.
5 Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
¡Cuán grande es nuestro Señor! ¡Su poder es inmenso! ¡Su conocimiento es infinito!
6 Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
El Señor ayuda a levantar a los agobiados, pero a los malvados los derriba.
7 Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
¡Canten con agradecimiento al Señor! ¡Canten alabanzas a Dios con arpa!
8 Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
Él cubre el cielo con nubes para traer lluvia a la tierra, y hace crecer el pasto en las colinas.
9 Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
Él alimenta a los animales, y a los cuervos cuando lo piden.
10 Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
El Señor no se complace de la fuera de caballos de guerra ni del poder humano.
11 Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
En cambio el Señor se alegra con quienes lo siguen, aquellos que ponen su confianza en su amor y fidelidad.
12 Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
¡Alaba al Señor, Jerusalén! ¡Sión, alaba a tu Dios!
13 Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
Él fortalece las rejas de las puertas de la ciudad, y bendice a los hijos que habitan contigo.
14 Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
Él mantiene las fronteras de tu nación seguras contra los ataques, y te provee del mejor trigo.
15 Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
Él envía sus órdenes por todo el mundo y de inmediato su voluntad es ejecutada.
16 Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
Él envía la nieve tan blanca como la lana, y esparce la escarcha de hielo como cenizas.
17 Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
Él envía el granizo como piedras. ¿Quién pudiera soportar el frío que él envía?
18 Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
Entonces con su voz de mando la hace derretir. Él sopla y el agua fluye.
19 Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
Él proclama su palabra a Jacob; sus principios y leyes a Israel.
20 Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.
Él no ha hecho estas cosas por ninguna otra nación, pues ellos no conocen sus leyes. ¡Alaben al Señor!

< Zabura 147 >