< Zabura 147 >
1 Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
Alleluia. Laudate Dominum quoniam bonus est psalmus: Deo nostro sit iucunda, decoraque laudatio.
2 Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
Aedificans Ierusalem Dominus: dispersiones Israelis congregabit.
3 Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
Qui sanat contritos corde: et alligat contritiones eorum.
4 Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
Qui numerat multitudinem stellarum: et omnibus eis nomina vocat.
5 Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
Magnus Dominus noster, et magna virtus eius: et sapientiae eius non est numerus.
6 Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
Suscipiens mansuetos Dominus: humilians autem peccatores usque ad terram.
7 Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
Praecinite Domino in confessione: psallite Deo nostro in cithara.
8 Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
Qui operit caelum nubibus: et parat terrae pluviam. Qui producit in montibus foenum: et herbam servituti hominum.
9 Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
Qui dat iumentis escam ipsorum: et pullis corvorum invocantibus eum.
10 Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
Non in fortitudine equi voluntatem habebit: nec in tibiis viri beneplacitum erit ei.
11 Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
Beneplacitum est Domino super timentes eum: et in eis, qui sperant super misericordia eius.
12 Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
Alleluia. Lauda Ierusalem Dominum: lauda Deum tuum Sion.
13 Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
Quoniam confortavit seras portarum tuarum: benedixit filiis tuis in te.
14 Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
Qui posuit fines tuos pacem: et adipe frumenti satiat te.
15 Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
Qui emittit eloquium suum terrae: velociter currit sermo eius.
16 Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
Qui dat nivem sicut lanam: nebulam sicut cinerem spargit,
17 Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
Mittit crystallum suam sicut buccellas: ante faciem frigoris eius quis sustinebit?
18 Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
Emittet verbum suum, et liquefaciet ea: flabit spiritus eius, et fluent aquae.
19 Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
Qui annunciat verbum suum Iacob: iustitias, et iudicia sua Israel.
20 Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.
Non fecit taliter omni nationi: et iudicia sua non manifestavit eis. Alleluia.