< Zabura 147 >
1 Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
主をほめたたえよ。われらの神をほめうたうことはよいことである。主は恵みふかい。さんびはふさわしいことである。
2 Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
主はエルサレムを築き、イスラエルの追いやられた者を集められる。
3 Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
主は心の打ち砕かれた者をいやし、その傷を包まれる。
4 Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
主はもろもろの星の数を定め、すべてそれに名を与えられる。
5 Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
われらの主は大いなる神、力も豊かであって、その知恵ははかりがたい。
6 Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
主はしえたげられた者をささえ、悪しき者を地に投げ捨てられる。
7 Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
主に感謝して歌え、琴にあわせてわれらの神をほめうたえ。
8 Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
主は雲をもって天をおおい、地のために雨を備え、もろもろの山に草をはえさせ、
9 Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
食物を獣に与え、また鳴く小がらすに与えられる。
10 Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
主は馬の力を喜ばれず、人の足をよみせられない。
11 Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
主はおのれを恐れる者とそのいつくしみを望む者とをよみせられる。
12 Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
エルサレムよ、主をほめたたえよ。シオンよ、あなたの神をほめたたえよ。
13 Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
主はあなたの門の貫の木を堅くし、あなたのうちにいる子らを祝福されるからである。
14 Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
主はあなたの国境を安らかにし、最も良い麦をもってあなたを飽かせられる。
15 Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
主はその戒めを地に下される。そのみ言葉はすみやかに走る。
16 Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
主は雪を羊の毛のように降らせ、霜を灰のようにまかれる。
17 Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
主は氷をパンくずのように投げうたれる。だれがその寒さに耐えることができましょうか。
18 Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
主はみ言葉を下してこれを溶かし、その風を吹かせられると、もろもろの水は流れる。
19 Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
主はそのみ言葉をヤコブに示し、そのもろもろの定めと、おきてとをイスラエルに示される。
20 Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.
主はいずれの国民をも、このようにはあしらわれなかった。彼らは主のもろもろのおきてを知らない。主をほめたたえよ。