< Zabura 147 >
1 Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
Lobet Jehova! [Hallelujah!] denn es ist gut, unseren Gott zu besingen; denn es ist lieblich, es geziemt sich Lobgesang.
2 Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
Jehova baut Jerusalem, die Vertriebenen Israels sammelt er.
3 Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
Der da heilt, die zerbrochenen Herzens sind, und ihre Wunden verbindet;
4 Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
Der da zählt die Zahl der Sterne, sie alle nennt mit Namen.
5 Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
Groß ist unser Herr, und groß [O. reich] an Macht; seiner Einsicht ist kein Maß. [Eig. keine Zahl]
6 Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
Jehova hält aufrecht die Elenden; er erniedrigt bis zur Erde die Gesetzlosen.
7 Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
Stimmet Jehova einen Lobgesang [O. Danklied] an, singet Psalmen unserem Gott mit der Laute!
8 Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
Ihm, der die Himmel mit Wolken bedeckt, der Regen bereitet für die Erde, der Gras sprossen läßt auf den Bergen;
9 Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
Der dem Vieh sein Futter gibt, den jungen Raben, die da rufen.
10 Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
Er hat nicht Lust an der Stärke des Rosses, noch Gefallen an den Beinen des Mannes;
11 Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
Jehova hat Gefallen an denen, die ihn fürchten, an denen, die auf seine Güte harren.
12 Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
Rühme, Jerusalem, Jehova! lobe, Zion, deinen Gott!
13 Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
Denn er hat befestigt die Riegel deiner Tore, hat deine Kinder gesegnet in deiner Mitte;
14 Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
Er, der Frieden stellt in deine Grenzen, dich sättigt mit dem Fette des Weizens;
15 Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
Der seinen Befehl auf die Erde sendet: sehr schnell läuft sein Wort;
16 Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
Der Schnee gibt wie Wolle, Reif wie Asche streut;
17 Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
Der sein Eis [d. h. den Hagel] wirft wie Brocken: wer kann bestehen vor seinem Frost?
18 Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
Er sendet sein Wort und schmelzt sie; er läßt seinen Wind wehen: es rieseln die Wasser.
19 Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
Er verkündet [O. verkündete] Jakob sein Wort, Israel seine Satzungen und seine Rechte.
20 Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.
Keiner Nation hat er also getan; und die Rechte, sie haben sie nicht gekannt. [O. kennen sie nicht] Lobet Jehova! [Hallelujah!]