< Zabura 147 >

1 Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
Louez l'Eternel; car c'est une chose bonne de psalmodier à notre Dieu, car c'est une chose agréable; [et] la louange en est bienséante.
2 Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
L'Eternel est celui qui bâtit Jérusalem; il rassemblera ceux d'Israël qui sont dispersés çà et là.
3 Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
Il guérit ceux qui sont brisés de cœur, et il bande leurs plaies.
4 Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
Il compte le nombre des étoiles; il les appelle toutes par leur nom.
5 Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
Notre Seigneur est grand et d'une grande puissance, son intelligence est incompréhensible.
6 Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
L'Eternel maintient les débonnaires, [mais] il abaisse les méchants jusqu’en terre.
7 Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
Chantez à l'Eternel avec action de grâces, vous entre-répondant les uns aux autres; psalmodiez avec la harpe à notre Dieu;
8 Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
Qui couvre de nuées les cieux; qui apprête la pluie pour la terre; qui fait produire le foin aux montagnes;
9 Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
Qui donne la pâture au bétail, et aux petits du corbeau, qui crient.
10 Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
Il ne prend point de plaisir en la force du cheval; il ne fait point cas des jambières de l'homme.
11 Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
L'Eternel met son affection en ceux qui le craignent, en ceux qui s'attendent à sa bonté.
12 Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
Jérusalem, loue l'Eternel; Sion, loue ton Dieu.
13 Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
Car il a renforcé les barres de tes portes; il a béni tes enfants au milieu de toi.
14 Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
C'est lui qui rend paisibles tes contrées, et qui te rassasie de la mœlle du froment.
15 Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
C'est lui qui envoie sa parole sur la terre, [et] sa parole court avec beaucoup de vitesse.
16 Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
C'est lui qui donne la neige comme [des flocons] de laine, et qui répand la bruine comme de la cendre.
17 Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
C'est lui qui jette sa glace comme par morceaux; et qui est-ce qui pourra durer devant sa froidure?
18 Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
Il envoie sa parole, et les fait fondre; il fait souffler son vent, [et] les eaux s'écoulent.
19 Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
Il déclare ses paroles à Jacob, et ses statuts et ses ordonnances à Israël.
20 Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.
Il n'a pas fait ainsi à toutes les nations, c'est pourquoi elles ne connaissent point ses ordonnances. Louez l'Eternel.

< Zabura 147 >