< Zabura 147 >

1 Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
Louez Yah, car il est bon de chanter les louanges de notre Dieu; car il est agréable et convenable de le louer.
2 Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
Yahvé bâtit Jérusalem. Il rassemble les exclus d'Israël.
3 Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
Il guérit les cœurs brisés, et panse leurs plaies.
4 Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
Il compte le nombre d'étoiles. Il les appelle tous par leur nom.
5 Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
Grand est notre Seigneur, et puissant en puissance. Sa compréhension est infinie.
6 Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
Yahvé soutient les humbles. Il fait tomber les méchants sur le sol.
7 Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
Chantez à Yahvé avec reconnaissance. Chantez les louanges de notre Dieu sur la harpe,
8 Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
qui couvre le ciel de nuages, qui prépare la pluie pour la terre, qui fait pousser l'herbe sur les montagnes.
9 Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
Il fournit la nourriture pour le bétail, et pour les jeunes corbeaux quand ils appellent.
10 Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
Il ne se réjouit pas de la force du cheval. Il ne prend aucun plaisir dans les jambes d'un homme.
11 Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
Yahvé prend plaisir à ceux qui le craignent, en ceux qui espèrent en sa bonté.
12 Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
Loue Yahvé, Jérusalem! Louez votre Dieu, Sion!
13 Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
Car il a renforcé les barres de tes portes. Il a béni vos enfants en vous.
14 Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
Il fait régner la paix dans tes frontières. Il vous remplit avec le meilleur du blé.
15 Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
Il envoie son commandement à la terre. Sa parole court très vite.
16 Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
Il donne de la neige comme de la laine, et disperse le givre comme des cendres.
17 Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
Il fait tomber sa grêle comme des cailloux. Qui peut se tenir devant son froid?
18 Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
Il envoie sa parole, et les fait fondre. Il fait souffler son vent, et les eaux coulent.
19 Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
Il montre sa parole à Jacob, ses lois et ses ordonnances à Israël.
20 Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.
Il n'a pas fait cela pour n'importe quelle nation. Ils ne connaissent pas ses ordonnances. Louez Yah!

< Zabura 147 >