< Zabura 147 >

1 Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
Praise ye Jah! For [it is] good to praise our God, For pleasant — comely [is] praise.
2 Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
Building Jerusalem [is] Jehovah, The driven away of Israel He gathereth.
3 Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
Who is giving healing to the broken of heart, And is binding up their griefs.
4 Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
Appointing the number of the stars, To all them He giveth names.
5 Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
Great [is] our Lord, and abundant in power, Of His understanding there is no narration.
6 Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
Jehovah is causing the meek to stand, Making low the wicked unto the earth.
7 Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
Answer ye to Jehovah with thanksgiving, Sing ye to our God with a harp.
8 Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
Who is covering the heavens with clouds, Who is preparing for the earth rain, Who is causing grass to spring up [on] mountains,
9 Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
Giving to the beast its food, To the young of the ravens that call.
10 Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
Not in the might of the horse doth He delight, Not in the legs of a man is He pleased.
11 Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
Jehovah is pleased with those fearing Him, With those waiting for His kindness.
12 Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
Glorify, O Jerusalem, Jehovah, Praise thy God, O Zion.
13 Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
For He did strengthen the bars of thy gates, He hath blessed thy sons in thy midst.
14 Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
Who is making thy border peace, [With] the fat of wheat He satisfieth Thee.
15 Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
Who is sending forth His saying [on] earth, Very speedily doth His word run.
16 Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
Who is giving snow like wool, Hoar-frost as ashes He scattereth.
17 Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
Casting forth His ice like morsels, Before His cold who doth stand?
18 Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
He sendeth forth His word and melteth them, He causeth His wind to blow — the waters flow.
19 Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
Declaring His words to Jacob, His statutes and His judgments to Israel.
20 Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.
He hath not done so to any nation, As to judgments, they have not known them. Praise ye Jah!

< Zabura 147 >