< Zabura 147 >

1 Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
Hallelujah; for it is good to sing praises unto our God; for it is pleasant, and praise is comely.
2 Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
The LORD doth build up Jerusalem, He gathereth together the dispersed of Israel;
3 Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
Who healeth the broken in heart, and bindeth up their wounds.
4 Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
He counteth the number of the stars; He giveth them all their names.
5 Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
Great is our Lord, and mighty in power; His understanding is infinite.
6 Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
The LORD upholdeth the humble; He bringeth the wicked down to the ground.
7 Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
Sing unto the LORD with thanksgiving, sing praises upon the harp unto our God;
8 Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
Who covereth the heaven with clouds, who prepareth rain for the earth, who maketh the mountains to spring with grass.
9 Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
He giveth to the beast his food, and to the young ravens which cry.
10 Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
He delighteth not in the strength of the horse; He taketh no pleasure in the legs of a man.
11 Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
The LORD taketh pleasure in them that fear Him, in those that wait for His mercy.
12 Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
Glorify the LORD, O Jerusalem; praise thy God, O Zion.
13 Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
For He hath made strong the bars of thy gates; He hath blessed thy children within thee.
14 Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
He maketh thy borders peace; He giveth thee in plenty the fat of wheat.
15 Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
He sendeth out His commandment upon earth; His word runneth very swiftly.
16 Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
He giveth snow like wool; He scattereth the hoar-frost like ashes.
17 Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
He casteth forth His ice like crumbs; who can stand before His cold?
18 Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
He sendeth forth His word, and melteth them; He causeth His wind to blow, and the waters flow.
19 Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
He declareth His word unto Jacob, His statutes and His ordinances unto Israel.
20 Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.
He hath not dealt so with any nation; and as for His ordinances, they have not known them. Hallelujah.

< Zabura 147 >