< Zabura 147 >

1 Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
Praise ye the Lord, for it is good to sing vnto our God: for it is a pleasant thing, and praise is comely.
2 Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
The Lord doth builde vp Ierusalem, and gather together the dispersed of Israel.
3 Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
He healeth those that are broken in heart, and bindeth vp their sores.
4 Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
He counteth the nomber of the starres, and calleth them all by their names.
5 Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
Great is our Lord, and great is his power: his wisdome is infinite.
6 Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
The Lord relieueth the meeke, and abaseth the wicked to the ground.
7 Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
Sing vnto the Lord with prayse: sing vpon the harpe vnto our God,
8 Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
Which couereth the heauen with cloudes, and prepareth raine for the earth, and maketh the grasse to growe vpon the mountaines:
9 Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
Which giueth to beasts their foode, and to the yong rauens that crie.
10 Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
He hath not pleasure in the strength of an horse, neither delighteth he in the legs of man.
11 Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
But the Lord deliteth in them that feare him, and attende vpon his mercie.
12 Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
Prayse the Lord, O Ierusalem: prayse thy God, O Zion.
13 Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
For he hath made the barres of thy gates strong, and hath blessed thy children within thee.
14 Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
He setteth peace in thy borders, and satisfieth thee with the floure of wheate.
15 Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
He sendeth foorth his commandement vpon earth, and his worde runneth very swiftly.
16 Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
He giueth snowe like wooll, and scattereth the hoare frost like ashes.
17 Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
He casteth foorth his yce like morsels: who can abide the colde thereof?
18 Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
He sendeth his worde and melteth them: he causeth his winde to blowe, and the waters flowe.
19 Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
He sheweth his word vnto Iaakob, his statutes and his iudgements vnto Israel.
20 Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.
He hath not dealt so with euery nation, neither haue they knowen his iudgements. Prayse ye the Lord.

< Zabura 147 >