< Zabura 147 >
1 Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
Praise ye the Lord, because psalm is good: to our God be joyful and comely praise.
2 Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
The Lord buildeth up Jerusalem: he will gather together the dispersed of Israel.
3 Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
Who healeth the broken of heart, and bindeth up their bruises.
4 Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
Who telleth the number of the stars: and calleth them all by their names.
5 Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
Great is our Lord, and great is his power: and of his wisdom there is no number.
6 Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
The Lord lifteth up the meek, and bringeth the wicked down even to the ground.
7 Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
Sing ye to the Lord with praise: sing to our God upon the harp.
8 Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
Who covereth the heaven with clouds, and prepareth rain for the earth. Who maketh grass to grow on the mountains, and herbs for the service of men.
9 Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
Who giveth to beasts their food: and to the young ravens that call upon him.
10 Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
He shall not delight in the strength of the horse: nor take pleasure in the legs of a man.
11 Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
The Lord taketh pleasure in them that fear him: and in them that hope in his mercy.
12 Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
Praise the Lord, O Jerusalem: praise thy God, O Sion.
13 Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
Because he hath strengthened the bolts of thy gates, he hath blessed thy children within thee.
14 Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
Who hath placed peace in thy borders: and filleth thee with the fat of corn.
15 Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
Who sendeth forth his speech to the earth: his word runneth swiftly.
16 Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
Who giveth snow like wool: scattereth mists like ashes.
17 Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
He sendeth his crystal like morsels: who shall stand before the face of his cold?
18 Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
He shall send out his word, and shall melt them: his wind shall blow, and the waters shall run.
19 Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
Who declareth his word to Jacob: his justices and his judgments to Israel.
20 Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.
He hath not done in like manner to every nation: and his judgments he hath not made manifest to them. Alleluia.