< Zabura 147 >

1 Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
Give praise to the Lord; for it is good to make melody to our God; praise is pleasing and beautiful.
2 Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
The Lord is building up Jerusalem; he makes all the outlaws of Israel come together.
3 Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
He makes the broken-hearted well, and puts oil on their wounds.
4 Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
He sees the number of the stars; he gives them all their names.
5 Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
Great is our Lord, and great his power; there is no limit to his wisdom.
6 Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
The Lord gives help to the poor in spirit; but he sends sinners down in shame.
7 Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
Make songs of praise to the Lord; make melody to our God with instruments of music.
8 Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
By his hand the heaven is covered with clouds and rain is stored up for the earth; he makes the grass tall on the mountains.
9 Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
He gives food to every beast, and to the young ravens in answer to their cry.
10 Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
He has no delight in the strength of a horse; he takes no pleasure in the legs of a man.
11 Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
The Lord takes pleasure in his worshippers, and in those whose hope is in his mercy.
12 Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
Give praise to the Lord, O Jerusalem; give praise to your God, O Zion.
13 Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
He has made strong the iron bands of your doors; he has sent blessings on your children inside your walls.
14 Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
He gives peace in all your land, making your stores full of fat grain.
15 Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
He sends out his orders to the earth; his word goes out quickly.
16 Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
He gives snow like wool; he sends out ice-drops like dust.
17 Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
He sends down ice like raindrops: water is made hard by his cold.
18 Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
At the outgoing of his word, the ice is turned to water; when he sends out his wind, there is a flowing of waters.
19 Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
He makes his word clear to Jacob, teaching Israel his laws and his decisions.
20 Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.
He has not done these things for any other nation: and as for his laws, they have no knowledge of them. Let the Lord be praised.

< Zabura 147 >